< Zabura 114 >

1 Sa’ad da Isra’ila ya fito daga Masar, gidan Yaƙub daga mutane masu baƙon harshe,
Alleluia. In exitu Israel de Ægypto, domus Iacob de populo barbaro:
2 Yahuda ya zama wuri mai tsarki na Allah, Isra’ila mallakarsa.
Facta est Iudæa sanctificatio eius, Israel potestas eius.
3 Teku ya kalla ya kuma gudu, Urdun ya juye da baya;
Mare vidit, et fugit: Iordanis conversus est retrorsum.
4 duwatsu suka yi tsalle kamar raguna, tuddai kamar tumaki.
Montes exultaverunt ut arietes: et colles sicut agni ovium.
5 Me ya sa, ya teku, kika gudu, Ya Urdun, ka juya baya,
Quid est tibi mare quod fugisti: et tu Iordanis, quia conversus es retrorsum?
6 ku duwatsu, kuka yi tsalle kamar raguna, ku tuddai, kamar tumaki?
Montes exultastis sicut arietes, et colles sicut agni ovium?
7 Ki yi rawar jiki, ya duniya, a gaban Ubangiji, a gaban Allah na Yaƙub,
A facie Domini mota est terra, a facie Dei Iacob.
8 wanda ya juye dutse ya zama tafki, dutse mai ƙarfi zuwa maɓulɓulan ruwa.
Qui convertit petram in stagna aquarum, et rupem in fontes aquarum.

< Zabura 114 >