< Zabura 114 >

1 Sa’ad da Isra’ila ya fito daga Masar, gidan Yaƙub daga mutane masu baƙon harshe,
Quand Israël sortit de l'Egypte, Quand la maison de Jacob se sépara d'un peuple barbare,
2 Yahuda ya zama wuri mai tsarki na Allah, Isra’ila mallakarsa.
Juda devint le sanctuaire de l'Éternel, Et Israël son empire.
3 Teku ya kalla ya kuma gudu, Urdun ya juye da baya;
A la vue du peuple de Dieu, la mer s'enfuit; Le Jourdain retourna en arrière.
4 duwatsu suka yi tsalle kamar raguna, tuddai kamar tumaki.
Les montagnes bondirent comme des béliers, Et les collines comme des agneaux.
5 Me ya sa, ya teku, kika gudu, Ya Urdun, ka juya baya,
Qu'avais-tu, ô mer, pour t'enfuir, Et toi, Jourdain, pour retourner en arrière?
6 ku duwatsu, kuka yi tsalle kamar raguna, ku tuddai, kamar tumaki?
Pourquoi bondir comme des béliers, ô montagnes. Et vous, collines, comme des agneaux?
7 Ki yi rawar jiki, ya duniya, a gaban Ubangiji, a gaban Allah na Yaƙub,
Terre, tremble devant le Seigneur, Devant le Dieu de Jacob,
8 wanda ya juye dutse ya zama tafki, dutse mai ƙarfi zuwa maɓulɓulan ruwa.
Qui change le rocher en nappe d'eau, Le granit en source jaillissante.

< Zabura 114 >