< Zabura 114 >
1 Sa’ad da Isra’ila ya fito daga Masar, gidan Yaƙub daga mutane masu baƙon harshe,
When Israel left Egypt, the house of Jacob from a people who spoke a foreign language,
2 Yahuda ya zama wuri mai tsarki na Allah, Isra’ila mallakarsa.
Judah became his holy place, Israel his kingdom.
3 Teku ya kalla ya kuma gudu, Urdun ya juye da baya;
The sea looked and fled; the Jordan turned back.
4 duwatsu suka yi tsalle kamar raguna, tuddai kamar tumaki.
The mountains skipped like rams, the hills skipped like lambs.
5 Me ya sa, ya teku, kika gudu, Ya Urdun, ka juya baya,
Why did you flee, sea? Jordan, why did you turn back?
6 ku duwatsu, kuka yi tsalle kamar raguna, ku tuddai, kamar tumaki?
Mountains, why did you skip like rams? You little hills, why did you skip like lambs?
7 Ki yi rawar jiki, ya duniya, a gaban Ubangiji, a gaban Allah na Yaƙub,
Tremble, earth, before the Lord, at the presence of the God of Jacob.
8 wanda ya juye dutse ya zama tafki, dutse mai ƙarfi zuwa maɓulɓulan ruwa.
He turned the rock into a pool of water, the hard rock into a spring of water.