< Zabura 114 >

1 Sa’ad da Isra’ila ya fito daga Masar, gidan Yaƙub daga mutane masu baƙon harshe,
When Israel went out of Egypt, Jacob’s house from a barbarous people,
2 Yahuda ya zama wuri mai tsarki na Allah, Isra’ila mallakarsa.
God chose Judah for himself, Israel became his kingdom.
3 Teku ya kalla ya kuma gudu, Urdun ya juye da baya;
The sea saw it, and fled, Jordan river ran backwards.
4 duwatsu suka yi tsalle kamar raguna, tuddai kamar tumaki.
Mountains skipped like rams, hills like the young of the flock.
5 Me ya sa, ya teku, kika gudu, Ya Urdun, ka juya baya,
Why, sea, do you flee? Jordan, why run backwards?
6 ku duwatsu, kuka yi tsalle kamar raguna, ku tuddai, kamar tumaki?
Mountains, why skip ram-like? Why, hills, like the young of the flock?
7 Ki yi rawar jiki, ya duniya, a gaban Ubangiji, a gaban Allah na Yaƙub,
Earth, tremble before the Lord, at the presence of Jacob’s God,
8 wanda ya juye dutse ya zama tafki, dutse mai ƙarfi zuwa maɓulɓulan ruwa.
who turns rocks into pools of water, and flint into fountains of water.

< Zabura 114 >