< Zabura 114 >
1 Sa’ad da Isra’ila ya fito daga Masar, gidan Yaƙub daga mutane masu baƙon harshe,
When Israel came forth from Egypt, The house of Jacob from a people of strange language,
2 Yahuda ya zama wuri mai tsarki na Allah, Isra’ila mallakarsa.
Judah was his sanctuary, And Israel his dominion.
3 Teku ya kalla ya kuma gudu, Urdun ya juye da baya;
The sea beheld, and fled; The Jordan turned back.
4 duwatsu suka yi tsalle kamar raguna, tuddai kamar tumaki.
The mountains skipped like rams, And the hills like lambs.
5 Me ya sa, ya teku, kika gudu, Ya Urdun, ka juya baya,
What aileth thee, O thou sea! that thou fleest? Thou, Jordan, that thou runnest back?
6 ku duwatsu, kuka yi tsalle kamar raguna, ku tuddai, kamar tumaki?
Ye mountains, that ye skip like rams, And ye hills like lambs?
7 Ki yi rawar jiki, ya duniya, a gaban Ubangiji, a gaban Allah na Yaƙub,
Tremble, O earth! at the presence of the Lord, At the presence of the God of Jacob;
8 wanda ya juye dutse ya zama tafki, dutse mai ƙarfi zuwa maɓulɓulan ruwa.
Who turned the rock into a standing lake, And the flint into a fountain of water!