< Zabura 114 >
1 Sa’ad da Isra’ila ya fito daga Masar, gidan Yaƙub daga mutane masu baƙon harshe,
When Israel came forth out of Egypt, the house of Jacob from a people of strange language;
2 Yahuda ya zama wuri mai tsarki na Allah, Isra’ila mallakarsa.
Judah became His sanctuary, Israel His dominion.
3 Teku ya kalla ya kuma gudu, Urdun ya juye da baya;
The sea saw it, and fled; the Jordan turned backward.
4 duwatsu suka yi tsalle kamar raguna, tuddai kamar tumaki.
The mountains skipped like rams, the hills like young sheep.
5 Me ya sa, ya teku, kika gudu, Ya Urdun, ka juya baya,
What aileth thee, O thou sea, that thou fleest? thou Jordan, that thou turnest backward?
6 ku duwatsu, kuka yi tsalle kamar raguna, ku tuddai, kamar tumaki?
Ye mountains, that ye skip like rams; ye hills, like young sheep?
7 Ki yi rawar jiki, ya duniya, a gaban Ubangiji, a gaban Allah na Yaƙub,
Tremble, thou earth, at the presence of the Lord, at the presence of the God of Jacob;
8 wanda ya juye dutse ya zama tafki, dutse mai ƙarfi zuwa maɓulɓulan ruwa.
Who turned the rock into a pool of water, the flint into a fountain of waters.