< Zabura 114 >

1 Sa’ad da Isra’ila ya fito daga Masar, gidan Yaƙub daga mutane masu baƙon harshe,
When Israel went out of Egypt, the house of Jacob from a barbarous people:
2 Yahuda ya zama wuri mai tsarki na Allah, Isra’ila mallakarsa.
Judea made his sanctuary, Israel his dominion.
3 Teku ya kalla ya kuma gudu, Urdun ya juye da baya;
The sea saw and fled: Jordan was turned back.
4 duwatsu suka yi tsalle kamar raguna, tuddai kamar tumaki.
The mountains skipped like rams, and the hills like the lambs of the flock.
5 Me ya sa, ya teku, kika gudu, Ya Urdun, ka juya baya,
What ailed thee, O thou sea, that thou didst flee: and thou, O Jordan, that thou wast turned back?
6 ku duwatsu, kuka yi tsalle kamar raguna, ku tuddai, kamar tumaki?
Ye mountains, that ye skipped like rams, and ye hills, like lambs of the flock?
7 Ki yi rawar jiki, ya duniya, a gaban Ubangiji, a gaban Allah na Yaƙub,
At the presence of the Lord the earth was moved, at the presence of the God of Jacob:
8 wanda ya juye dutse ya zama tafki, dutse mai ƙarfi zuwa maɓulɓulan ruwa.
Who turned the rock into pools of water, and the stony hill into fountains of waters.

< Zabura 114 >