< Zabura 114 >

1 Sa’ad da Isra’ila ya fito daga Masar, gidan Yaƙub daga mutane masu baƙon harshe,
以色列出了埃及, 雅各家离开说异言之民;
2 Yahuda ya zama wuri mai tsarki na Allah, Isra’ila mallakarsa.
那时,犹大为主的圣所, 以色列为他所治理的国度。
3 Teku ya kalla ya kuma gudu, Urdun ya juye da baya;
沧海看见就奔逃; 约旦河也倒流。
4 duwatsu suka yi tsalle kamar raguna, tuddai kamar tumaki.
大山踊跃,如公羊; 小山跳舞,如羊羔。
5 Me ya sa, ya teku, kika gudu, Ya Urdun, ka juya baya,
沧海啊,你为何奔逃? 约旦哪,你为何倒流?
6 ku duwatsu, kuka yi tsalle kamar raguna, ku tuddai, kamar tumaki?
大山哪,你为何踊跃,如公羊? 小山哪,你为何跳舞,如羊羔?
7 Ki yi rawar jiki, ya duniya, a gaban Ubangiji, a gaban Allah na Yaƙub,
大地啊,你因见主的面, 就是雅各 神的面,便要震动。
8 wanda ya juye dutse ya zama tafki, dutse mai ƙarfi zuwa maɓulɓulan ruwa.
他叫磐石变为水池, 叫坚石变为泉源。

< Zabura 114 >