< Zabura 112 >

1 Yabi Ubangiji. Mai albarka ne mutumin da yake tsoron Ubangiji, wanda yakan sami farin ciki mai girma a umarnansa.
Алілу́я!
2 ’Ya’yansa za su zama manya a ƙasar; tsaran masu aikata gaskiya za su sami albarka.
Буде си́льним насі́ння його на землі, буде поблагосло́влений рід безневи́нних!
3 Wadata da arziki suna a cikin gidansa, adalcinsa zai dawwama har abada.
Багатство й достаток у домі його, а правда його пробува́є навіки!
4 Ko a cikin duhu haske kan haskaka wa mai aikata gaskiya, mai alheri mai tausayi da kuma mai adalci.
Світло схо́дить у те́мряві для справедливих, — Він ласка́вий, і милости́вий, і праведний!
5 Abu mai kyau zai zo masa shi da yake kyauta yake kuma ba da bashi hannu sake, shi da yake yin al’amuransa cikin gaskiya.
Добрий муж милости́вий та позичає, уде́ржує справи свої справедливістю,
6 Tabbatacce ba zai taɓa jijjigu ba; za a tuna da mai adalci har abada.
і наві́ки він не захита́ється, — у вічній па́м'яті праведний бу́де!
7 Ba zai ji tsoron labari marar daɗi ba; zuciyarsa tsayayyiya ce, tana dogara ga Ubangiji.
Не боїться він зві́стки лихої, його серце міцне́, наді́ю складає на Господа!
8 Zuciyarsa tana da kāriya, ba zai ji tsoro ba; a ƙarshe zai zama mai nasara a kan maƙiyansa.
Умі́цнене серце його не боїться, бо він бачить нещастя поміж ворога́ми своїми!
9 Ya rarraba kyautansa ga matalauta, adalcinsa zai dawwama har abada; za a ɗaga ƙahonsa sama da bangirma.
Він щедро убогим дає, його правда наві́ки стоїть, його ріг підіймається в славі!
10 Mugun mutum zai gani yă kuma yi fushi, zai ciza haƙora yă kuma lalace; sha’awace-sha’awacen mugaye za su zo ga ƙarshe.
Це бачить безбожний та гні́вається, скрего́че зубами своїми та та́не. Бажа́ння безбожних загине!

< Zabura 112 >