< Zabura 112 >

1 Yabi Ubangiji. Mai albarka ne mutumin da yake tsoron Ubangiji, wanda yakan sami farin ciki mai girma a umarnansa.
Deje que el Señor sea alabado. Feliz es el hombre que le da honor al Señor y se deleita en sus leyes.
2 ’Ya’yansa za su zama manya a ƙasar; tsaran masu aikata gaskiya za su sami albarka.
Su simiente será fuerte en la tierra; las bendiciones estarán en la generación de los rectos.
3 Wadata da arziki suna a cikin gidansa, adalcinsa zai dawwama har abada.
Una tienda de riquezas estará en su casa, y su justicia será para siempre.
4 Ko a cikin duhu haske kan haskaka wa mai aikata gaskiya, mai alheri mai tausayi da kuma mai adalci.
Para el recto hay una luz que brilla en la oscuridad; él está lleno de gracia y compasión.
5 Abu mai kyau zai zo masa shi da yake kyauta yake kuma ba da bashi hannu sake, shi da yake yin al’amuransa cikin gaskiya.
Todo está bien para el hombre que es amable y da libremente a los demás; él hará bien a su causa cuando sea juzgado.
6 Tabbatacce ba zai taɓa jijjigu ba; za a tuna da mai adalci har abada.
Él nunca será movido; el recuerdo del recto vivirá para siempre.
7 Ba zai ji tsoron labari marar daɗi ba; zuciyarsa tsayayyiya ce, tana dogara ga Ubangiji.
No temerá las malas noticias; su corazón está firme, porque su esperanza está en el Señor.
8 Zuciyarsa tana da kāriya, ba zai ji tsoro ba; a ƙarshe zai zama mai nasara a kan maƙiyansa.
Su corazón está descansando seguro, no tendrá miedo, hasta que vea con problemas a sus enemigos.
9 Ya rarraba kyautansa ga matalauta, adalcinsa zai dawwama har abada; za a ɗaga ƙahonsa sama da bangirma.
Él ha dado con las manos abiertas a los pobres; su justicia es para siempre; su frente se levantará con honor.
10 Mugun mutum zai gani yă kuma yi fushi, zai ciza haƙora yă kuma lalace; sha’awace-sha’awacen mugaye za su zo ga ƙarshe.
El pecador lo verá y se irritará; él será consumido por la envidia; el deseo de los malhechores quedará en nada.

< Zabura 112 >