< Zabura 112 >
1 Yabi Ubangiji. Mai albarka ne mutumin da yake tsoron Ubangiji, wanda yakan sami farin ciki mai girma a umarnansa.
Halleluja! Salig er den mann som frykter Herren, som har sin store lyst i hans bud.
2 ’Ya’yansa za su zama manya a ƙasar; tsaran masu aikata gaskiya za su sami albarka.
Hans avkom skal være mektig på jorden; de opriktiges slekt skal velsignes.
3 Wadata da arziki suna a cikin gidansa, adalcinsa zai dawwama har abada.
Det er velstand og rikdom i hans hus, og hans rettferdighet står fast evindelig.
4 Ko a cikin duhu haske kan haskaka wa mai aikata gaskiya, mai alheri mai tausayi da kuma mai adalci.
Det går op et lys i mørket for de opriktige, for den som er nådig og barmhjertig og rettferdig.
5 Abu mai kyau zai zo masa shi da yake kyauta yake kuma ba da bashi hannu sake, shi da yake yin al’amuransa cikin gaskiya.
Lykkelig er den mann som forbarmer sig og låner ut; han hevder all sin sak i dommen.
6 Tabbatacce ba zai taɓa jijjigu ba; za a tuna da mai adalci har abada.
For han skal ikke rokkes evindelig; den rettferdige skal være i evig minne.
7 Ba zai ji tsoron labari marar daɗi ba; zuciyarsa tsayayyiya ce, tana dogara ga Ubangiji.
Han skal ikke frykte for nogen ond tidende; hans hjerte er fast, det setter sin lit til Herren.
8 Zuciyarsa tana da kāriya, ba zai ji tsoro ba; a ƙarshe zai zama mai nasara a kan maƙiyansa.
Hans hjerte er trygt; han frykter ikke, inntil han ser med lyst på sine fiender.
9 Ya rarraba kyautansa ga matalauta, adalcinsa zai dawwama har abada; za a ɗaga ƙahonsa sama da bangirma.
Han har strødd ut, han har gitt de fattige; hans rettferdighet står fast evindelig, hans horn skal ophøies med ære.
10 Mugun mutum zai gani yă kuma yi fushi, zai ciza haƙora yă kuma lalace; sha’awace-sha’awacen mugaye za su zo ga ƙarshe.
Den ugudelige skal se det og harmes, han skal skjære tenner og optæres; de ugudeliges attrå blir til intet.