< Zabura 112 >

1 Yabi Ubangiji. Mai albarka ne mutumin da yake tsoron Ubangiji, wanda yakan sami farin ciki mai girma a umarnansa.
Alleluia, Reversionis Aggæi, et Zachariæ. Beatus vir, qui timet Dominum: in mandatis eius volet nimis.
2 ’Ya’yansa za su zama manya a ƙasar; tsaran masu aikata gaskiya za su sami albarka.
Potens in terra erit semen eius: generatio rectorum benedicetur.
3 Wadata da arziki suna a cikin gidansa, adalcinsa zai dawwama har abada.
Gloria, et divitiæ in domo eius: et iustitia eius manet in sæculum sæculi.
4 Ko a cikin duhu haske kan haskaka wa mai aikata gaskiya, mai alheri mai tausayi da kuma mai adalci.
Exortum est in tenebris lumen rectis: misericors, et miserator, et iustus.
5 Abu mai kyau zai zo masa shi da yake kyauta yake kuma ba da bashi hannu sake, shi da yake yin al’amuransa cikin gaskiya.
Iucundus homo qui miseretur et commodat, disponet sermones suos in iudicio:
6 Tabbatacce ba zai taɓa jijjigu ba; za a tuna da mai adalci har abada.
quia in æternum non commovebitur.
7 Ba zai ji tsoron labari marar daɗi ba; zuciyarsa tsayayyiya ce, tana dogara ga Ubangiji.
In memoria æterna erit iustus: ab auditione mala non timebit. Paratum cor eius sperare in Domino,
8 Zuciyarsa tana da kāriya, ba zai ji tsoro ba; a ƙarshe zai zama mai nasara a kan maƙiyansa.
confirmatum est cor eius: non commovebitur donec despiciat inimicos suos.
9 Ya rarraba kyautansa ga matalauta, adalcinsa zai dawwama har abada; za a ɗaga ƙahonsa sama da bangirma.
Dispersit, dedit pauperibus: iustitia eius manet in sæculum sæculi, cornu eius exaltabitur in gloria.
10 Mugun mutum zai gani yă kuma yi fushi, zai ciza haƙora yă kuma lalace; sha’awace-sha’awacen mugaye za su zo ga ƙarshe.
Peccator videbit, et irascetur, dentibus suis fremet et tabescet: desiderium peccatorum peribit.

< Zabura 112 >