< Zabura 112 >
1 Yabi Ubangiji. Mai albarka ne mutumin da yake tsoron Ubangiji, wanda yakan sami farin ciki mai girma a umarnansa.
Louez l'Éternel! Heureux l'homme qui craint l'Éternel, qui prend tout son plaisir en ses commandements!
2 ’Ya’yansa za su zama manya a ƙasar; tsaran masu aikata gaskiya za su sami albarka.
Sa postérité sera puissante sur la terre; la race des hommes droits sera bénie.
3 Wadata da arziki suna a cikin gidansa, adalcinsa zai dawwama har abada.
L'abondance et la richesse seront dans sa maison, et sa justice subsiste à toujours.
4 Ko a cikin duhu haske kan haskaka wa mai aikata gaskiya, mai alheri mai tausayi da kuma mai adalci.
La lumière se lève dans les ténèbres pour l'homme droit; il est compatissant, miséricordieux et juste.
5 Abu mai kyau zai zo masa shi da yake kyauta yake kuma ba da bashi hannu sake, shi da yake yin al’amuransa cikin gaskiya.
Heureux l'homme qui est compatissant et qui prête; qui règle ses actions selon la justice!
6 Tabbatacce ba zai taɓa jijjigu ba; za a tuna da mai adalci har abada.
Car il ne sera jamais ébranlé; la mémoire du juste sera perpétuelle.
7 Ba zai ji tsoron labari marar daɗi ba; zuciyarsa tsayayyiya ce, tana dogara ga Ubangiji.
Il n'a pas à craindre les mauvaises nouvelles; son cœur est ferme, s'assurant en l'Éternel.
8 Zuciyarsa tana da kāriya, ba zai ji tsoro ba; a ƙarshe zai zama mai nasara a kan maƙiyansa.
Son cœur bien appuyé ne craindra point, jusqu'à ce qu'il ait reposé sa vue sur ses ennemis.
9 Ya rarraba kyautansa ga matalauta, adalcinsa zai dawwama har abada; za a ɗaga ƙahonsa sama da bangirma.
Il a répandu, il a donné aux pauvres; sa justice demeure à perpétuité; sa tête s'élève avec gloire.
10 Mugun mutum zai gani yă kuma yi fushi, zai ciza haƙora yă kuma lalace; sha’awace-sha’awacen mugaye za su zo ga ƙarshe.
Le méchant le voit, et en a du dépit; il grince les dents et se consume; le désir des méchants périra.