< Zabura 112 >
1 Yabi Ubangiji. Mai albarka ne mutumin da yake tsoron Ubangiji, wanda yakan sami farin ciki mai girma a umarnansa.
Louez Yah! Heureux l'homme qui craint Yahvé, qui se complaît dans ses commandements.
2 ’Ya’yansa za su zama manya a ƙasar; tsaran masu aikata gaskiya za su sami albarka.
Sa progéniture sera puissante dans le pays. La génération des hommes intègres sera bénie.
3 Wadata da arziki suna a cikin gidansa, adalcinsa zai dawwama har abada.
La richesse et les richesses sont dans sa maison. Sa justice est éternelle.
4 Ko a cikin duhu haske kan haskaka wa mai aikata gaskiya, mai alheri mai tausayi da kuma mai adalci.
La lumière se lève dans les ténèbres pour les justes, gracieux, miséricordieux et juste.
5 Abu mai kyau zai zo masa shi da yake kyauta yake kuma ba da bashi hannu sake, shi da yake yin al’amuransa cikin gaskiya.
Tout va bien pour l'homme qui traite avec bonté et qui prête. Il maintiendra sa cause dans le jugement.
6 Tabbatacce ba zai taɓa jijjigu ba; za a tuna da mai adalci har abada.
Car il ne sera jamais ébranlé. On se souviendra toujours des justes.
7 Ba zai ji tsoron labari marar daɗi ba; zuciyarsa tsayayyiya ce, tana dogara ga Ubangiji.
Il ne craindra pas les mauvaises nouvelles. Son cœur est inébranlable, il a confiance en Yahvé.
8 Zuciyarsa tana da kāriya, ba zai ji tsoro ba; a ƙarshe zai zama mai nasara a kan maƙiyansa.
Son cœur est affermi. Il n'aura pas peur à la fin quand il verra ses adversaires.
9 Ya rarraba kyautansa ga matalauta, adalcinsa zai dawwama har abada; za a ɗaga ƙahonsa sama da bangirma.
Il a dispersé, il a donné aux pauvres. Sa justice est éternelle. Sa corne sera exaltée avec honneur.
10 Mugun mutum zai gani yă kuma yi fushi, zai ciza haƙora yă kuma lalace; sha’awace-sha’awacen mugaye za su zo ga ƙarshe.
Les méchants le verront, et seront affligés. Il grincera des dents et se fondra. Le désir des méchants périra.