< Zabura 112 >

1 Yabi Ubangiji. Mai albarka ne mutumin da yake tsoron Ubangiji, wanda yakan sami farin ciki mai girma a umarnansa.
Praise the LORD! Blessed is the man who fears the LORD, who delights greatly in his commandments.
2 ’Ya’yansa za su zama manya a ƙasar; tsaran masu aikata gaskiya za su sami albarka.
His offspring will be mighty in the land. The generation of the upright will be blessed.
3 Wadata da arziki suna a cikin gidansa, adalcinsa zai dawwama har abada.
Wealth and riches are in his house. His righteousness endures forever.
4 Ko a cikin duhu haske kan haskaka wa mai aikata gaskiya, mai alheri mai tausayi da kuma mai adalci.
Light dawns in the darkness for the upright, gracious, merciful, and righteous.
5 Abu mai kyau zai zo masa shi da yake kyauta yake kuma ba da bashi hannu sake, shi da yake yin al’amuransa cikin gaskiya.
It is well with the man who deals graciously and lends. He will maintain his cause in judgment.
6 Tabbatacce ba zai taɓa jijjigu ba; za a tuna da mai adalci har abada.
For he will never be shaken. The righteous will be remembered forever.
7 Ba zai ji tsoron labari marar daɗi ba; zuciyarsa tsayayyiya ce, tana dogara ga Ubangiji.
He will not be afraid of evil news. His heart is steadfast, trusting in the LORD.
8 Zuciyarsa tana da kāriya, ba zai ji tsoro ba; a ƙarshe zai zama mai nasara a kan maƙiyansa.
His heart is established. He will not be afraid in the end when he sees his adversaries.
9 Ya rarraba kyautansa ga matalauta, adalcinsa zai dawwama har abada; za a ɗaga ƙahonsa sama da bangirma.
He has dispersed, he has given to the poor. His righteousness endures forever. His horn will be exalted with honor.
10 Mugun mutum zai gani yă kuma yi fushi, zai ciza haƙora yă kuma lalace; sha’awace-sha’awacen mugaye za su zo ga ƙarshe.
The wicked will see it, and be grieved. He shall gnash with his teeth, and melt away. The desire of the wicked will perish.

< Zabura 112 >