< Zabura 112 >

1 Yabi Ubangiji. Mai albarka ne mutumin da yake tsoron Ubangiji, wanda yakan sami farin ciki mai girma a umarnansa.
Praise Yahweh! (Happy are/He is pleased with) those who revere him, those who happily obey his commands.
2 ’Ya’yansa za su zama manya a ƙasar; tsaran masu aikata gaskiya za su sami albarka.
Their children will prosper in their land; and their descendants will be blessed [by God].
3 Wadata da arziki suna a cikin gidansa, adalcinsa zai dawwama har abada.
Their families [MTY] will be very wealthy [DOU], and [the results of] their righteous deeds will endure forever.
4 Ko a cikin duhu haske kan haskaka wa mai aikata gaskiya, mai alheri mai tausayi da kuma mai adalci.
Godly/Righteous people are [like] lights [SIM] that shine in the darkness on those who are kind, merciful and righteous.
5 Abu mai kyau zai zo masa shi da yake kyauta yake kuma ba da bashi hannu sake, shi da yake yin al’amuransa cikin gaskiya.
Things [will] go well for those who generously lend money to others and who conduct their businesses honestly.
6 Tabbatacce ba zai taɓa jijjigu ba; za a tuna da mai adalci har abada.
Righteous people will not be overwhelmed/worried/distressed [because of their troubles], and they will never be forgotten [by other people].
7 Ba zai ji tsoron labari marar daɗi ba; zuciyarsa tsayayyiya ce, tana dogara ga Ubangiji.
They are not afraid of [receiving] bad news; they confidently/completely trust in Yahweh.
8 Zuciyarsa tana da kāriya, ba zai ji tsoro ba; a ƙarshe zai zama mai nasara a kan maƙiyansa.
They are confident and not afraid, because they know that they will see [God defeat] their enemies.
9 Ya rarraba kyautansa ga matalauta, adalcinsa zai dawwama har abada; za a ɗaga ƙahonsa sama da bangirma.
They give things generously to poor/needy [people]; [the results of] their kind deeds will endure forever, and they [will] be exalted and honored.
10 Mugun mutum zai gani yă kuma yi fushi, zai ciza haƙora yă kuma lalace; sha’awace-sha’awacen mugaye za su zo ga ƙarshe.
Wicked people see those things and are angry; they gnash their teeth [angrily], but they [will] disappear [and die]. The [wicked] things that they want to do [will] never happen.

< Zabura 112 >