< Zabura 112 >

1 Yabi Ubangiji. Mai albarka ne mutumin da yake tsoron Ubangiji, wanda yakan sami farin ciki mai girma a umarnansa.
Praise Yah. Blessed is the man that feareth Yhwh, that delighteth greatly in his commandments.
2 ’Ya’yansa za su zama manya a ƙasar; tsaran masu aikata gaskiya za su sami albarka.
His seed shall be mighty upon earth: the generation of the upright shall be blessed.
3 Wadata da arziki suna a cikin gidansa, adalcinsa zai dawwama har abada.
Wealth and riches shall be in his house: and his righteousness endureth for ever.
4 Ko a cikin duhu haske kan haskaka wa mai aikata gaskiya, mai alheri mai tausayi da kuma mai adalci.
Unto the upright there ariseth light in the darkness: he is gracious, and full of compassion, and righteous.
5 Abu mai kyau zai zo masa shi da yake kyauta yake kuma ba da bashi hannu sake, shi da yake yin al’amuransa cikin gaskiya.
A good man sheweth favour, and lendeth: he will guide his affairs with discretion.
6 Tabbatacce ba zai taɓa jijjigu ba; za a tuna da mai adalci har abada.
Surely he shall not be moved for ever: the righteous shall be in everlasting remembrance.
7 Ba zai ji tsoron labari marar daɗi ba; zuciyarsa tsayayyiya ce, tana dogara ga Ubangiji.
He shall not be afraid of evil tidings: his heart is fixed, trusting in Yhwh.
8 Zuciyarsa tana da kāriya, ba zai ji tsoro ba; a ƙarshe zai zama mai nasara a kan maƙiyansa.
His heart is established, he shall not be afraid, until he see his desire upon his enemies.
9 Ya rarraba kyautansa ga matalauta, adalcinsa zai dawwama har abada; za a ɗaga ƙahonsa sama da bangirma.
He hath dispersed, he hath given to the poor; his righteousness endureth for ever; his horn shall be exalted with honour.
10 Mugun mutum zai gani yă kuma yi fushi, zai ciza haƙora yă kuma lalace; sha’awace-sha’awacen mugaye za su zo ga ƙarshe.
The wicked shall see it, and be grieved; he shall gnash with his teeth, and melt away: the desire of the wicked shall perish.

< Zabura 112 >