< Zabura 112 >

1 Yabi Ubangiji. Mai albarka ne mutumin da yake tsoron Ubangiji, wanda yakan sami farin ciki mai girma a umarnansa.
Alleluia. Blessed is the man that fears the Lord: he will delight greatly in his commandments.
2 ’Ya’yansa za su zama manya a ƙasar; tsaran masu aikata gaskiya za su sami albarka.
His seed shall be mighty in the earth: the generation of the upright shall be blessed.
3 Wadata da arziki suna a cikin gidansa, adalcinsa zai dawwama har abada.
Glory and riches shall be in his house; and his righteousness endures for evermore.
4 Ko a cikin duhu haske kan haskaka wa mai aikata gaskiya, mai alheri mai tausayi da kuma mai adalci.
To the upright light has sprung up in darkness: he is pitiful, and merciful, and righteous.
5 Abu mai kyau zai zo masa shi da yake kyauta yake kuma ba da bashi hannu sake, shi da yake yin al’amuransa cikin gaskiya.
The good man is he that pities and lends: he will direct his affairs with judgment.
6 Tabbatacce ba zai taɓa jijjigu ba; za a tuna da mai adalci har abada.
For he shall not be moved for ever; the righteous shall be in everlasting remembrance.
7 Ba zai ji tsoron labari marar daɗi ba; zuciyarsa tsayayyiya ce, tana dogara ga Ubangiji.
He shall not be afraid of [any] evil report: his heart is ready to trust in the Lord.
8 Zuciyarsa tana da kāriya, ba zai ji tsoro ba; a ƙarshe zai zama mai nasara a kan maƙiyansa.
His heart is established, he shall not fear, till he shall see [his desire] upon his enemies.
9 Ya rarraba kyautansa ga matalauta, adalcinsa zai dawwama har abada; za a ɗaga ƙahonsa sama da bangirma.
He has dispersed abroad; he has given to the poor; his righteousness endures for evermore: his horn shall be exalted with honour.
10 Mugun mutum zai gani yă kuma yi fushi, zai ciza haƙora yă kuma lalace; sha’awace-sha’awacen mugaye za su zo ga ƙarshe.
The sinner shall see and be angry, he shall gnash his teeth, and consume away: the desire of the sinner shall perish.

< Zabura 112 >