< Zabura 112 >

1 Yabi Ubangiji. Mai albarka ne mutumin da yake tsoron Ubangiji, wanda yakan sami farin ciki mai girma a umarnansa.
BOEIPA te thangthen uh. BOEIPA aka rhih tih a olpaek dongah bahoeng aka hmae hlang tah a yoethen.
2 ’Ya’yansa za su zama manya a ƙasar; tsaran masu aikata gaskiya za su sami albarka.
A tiingan te diklai ah a rhalh la om vetih, aka thuem kah cadilcahma tah a yoethen ni.
3 Wadata da arziki suna a cikin gidansa, adalcinsa zai dawwama har abada.
A im ah boeinah neh khuehtawn soep tih a duengnah a yoeyah la cak.
4 Ko a cikin duhu haske kan haskaka wa mai aikata gaskiya, mai alheri mai tausayi da kuma mai adalci.
Aka thuem ham tah a hmuep khuiah khaw thinphoei lungvatnah neh duengnah khosae te a thoeng pah.
5 Abu mai kyau zai zo masa shi da yake kyauta yake kuma ba da bashi hannu sake, shi da yake yin al’amuransa cikin gaskiya.
Hlang then loh a rhen tih a pu vaengah a ol te a tiktamnah neh a cangbam.
6 Tabbatacce ba zai taɓa jijjigu ba; za a tuna da mai adalci har abada.
A dueng la aka om tah kumhal ah poekkoepnah a om coeng dongah anih ngawntah kumhal duela tuen mahpawh.
7 Ba zai ji tsoron labari marar daɗi ba; zuciyarsa tsayayyiya ce, tana dogara ga Ubangiji.
BOEIPA dongah aka pangtung tih a lungbuei aka cikngae loh olthang thae te rhih mahpawh.
8 Zuciyarsa tana da kāriya, ba zai ji tsoro ba; a ƙarshe zai zama mai nasara a kan maƙiyansa.
A lungbuei a uep dongah a rhal rhoek te a hmuh vaengah rhih mahpawh.
9 Ya rarraba kyautansa ga matalauta, adalcinsa zai dawwama har abada; za a ɗaga ƙahonsa sama da bangirma.
Khodaeng rhoek ham a tael pah tih a paek. A duengnah he a yoeyah la a cak dongah a ki khaw thangpomnah neh a pomsang ni.
10 Mugun mutum zai gani yă kuma yi fushi, zai ciza haƙora yă kuma lalace; sha’awace-sha’awacen mugaye za su zo ga ƙarshe.
Halang loh a hmuh vaengah hue a sak ni. A no tak cakhaw halang kah hoehhamnah ngawntah yip milh ni.

< Zabura 112 >