< Zabura 111 >

1 Yabi Ubangiji. Zan ɗaukaka Ubangiji da dukan zuciyata a cikin majalisar masu aikata gaskiya da kuma a cikin taro.
¡Alaben al Señor! Le agradeceré a Él con todo mi corazón ante la congregación de los fieles.
2 Ayyukan Ubangiji da girma suke; dukan waɗanda suke farin ciki da su suna tunaninsu.
Todas las maravillas que el Señor ha hecho son estudiadas por quienes lo aman.
3 Ayyukansa masu ɗaukaka da kuma daraja ne, adalcinsa kuma zai dawwama har abada.
Su honor y majestad son revelados por sus actos; su bondad perdura para siempre.
4 Ya sa a tuna da abubuwa masu banmamaki nasa; Ubangiji mai alheri ne mai tausayi kuma.
Él quiere que todas las cosas que ha hecho sean recordadas; el Señor es amable y lleno de gracia.
5 Yana ba da abinci ga waɗanda suke tsoronsa; yakan tuna da alkawarinsa har abada.
Alimenta a los que lo respetan; siempre tiene presente el acuerdo que hizo.
6 Ya nuna wa mutanensa ikon ayyukansa, yana ba su ƙasashen waɗansu al’ummai.
Le demostró a su pueblos las maravillosas cosas que podía hacer al darles las tierras de otras naciones.
7 Ayyukan hannuwansa masu aminci ne da kuma gaskiya; dukan farillansa abin dogara ne.
Todo lo que hace es justo; y sus mandamientos son confiables.
8 Tsayayyu ne har abada abadin, ana yinsu cikin aminci da kuma gaskiya.
Permanecen sólidos para siempre. Estaba en lo correcto al decir lo que debía hacerse.
9 Yana ba da ceto ga mutanensa; ya kafa alkawarinsa har abada, tsarki da banrazana ne sunansa.
Liberó a su pueblo. Y ordenó que su pacto perdurará para siempre. ¡Su nombre es santo e imponente!
10 Tsoron Ubangiji ne mafarin hikima; dukan waɗanda suke bin farillansa suna da ganewa mai kyau. Gare shi ne madawwamin yabo.
El principio de la sabiduría es honrar al Señor. Los que siguen sus mandamientos les va bien. ¡Su alabanza permanece para siempre!

< Zabura 111 >