< Zabura 110 >

1 Ta Dawuda. Zabura ce. Ubangiji ya ce wa Ubangijina, “Zauna a hannun damana, sai na sa abokan gābanka su zama matashin sawunka.”
David psalmus dixit Dominus Domino meo sede a dextris meis donec ponam inimicos tuos scabillum pedum tuorum
2 Ubangiji zai fadada ikon sandan mulkinka daga Sihiyona za ka yi mulki a tsakiyar abokan gābanka.
virgam virtutis tuae emittet Dominus ex Sion dominare in medio inimicorum tuorum
3 Rundunarka za su so yin yaƙi a ranarka ta yaƙi. Saye cikin ɗaukaka mai tsarki, daga cikin ciki na safiya za ka karɓi raɓar ƙuruciyarka.
tecum principium in die virtutis tuae in splendoribus sanctorum ex utero ante luciferum genui te
4 Ubangiji ya rantse ba zai kuma canja zuciyarsa ba, “Kai firist ne har abada, bisa ga tsarin Melkizedek.”
iuravit Dominus et non paenitebit eum tu es sacerdos in aeternum secundum ordinem Melchisedech
5 Ubangiji yana a hannun damanka; zai murƙushe sarakuna a ranar fushinsa.
Dominus a dextris tuis confregit in die irae suae reges
6 Zai hukunta al’ummai, yana tarawa gawawwaki yana kuma murƙushe masu mulkin dukan duniya.
iudicabit in nationibus implebit cadavera conquassabit capita in terra multorum
7 Zai sha daga rafin da yake kusa da hanya; saboda haka zai ɗaga kansa sama.
de torrente in via bibet propterea exaltabit caput

< Zabura 110 >