< Zabura 110 >

1 Ta Dawuda. Zabura ce. Ubangiji ya ce wa Ubangijina, “Zauna a hannun damana, sai na sa abokan gābanka su zama matashin sawunka.”
Oracolo del Signore al mio Signore: «Siedi alla mia destra, finché io ponga i tuoi nemici a sgabello dei tuoi piedi». Di Davide. Salmo.
2 Ubangiji zai fadada ikon sandan mulkinka daga Sihiyona za ka yi mulki a tsakiyar abokan gābanka.
Lo scettro del tuo potere stende il Signore da Sion: «Domina in mezzo ai tuoi nemici.
3 Rundunarka za su so yin yaƙi a ranarka ta yaƙi. Saye cikin ɗaukaka mai tsarki, daga cikin ciki na safiya za ka karɓi raɓar ƙuruciyarka.
A te il principato nel giorno della tua potenza tra santi splendori; dal seno dell'aurora, come rugiada, io ti ho generato».
4 Ubangiji ya rantse ba zai kuma canja zuciyarsa ba, “Kai firist ne har abada, bisa ga tsarin Melkizedek.”
Il Signore ha giurato e non si pente: «Tu sei sacerdote per sempre al modo di Melchisedek».
5 Ubangiji yana a hannun damanka; zai murƙushe sarakuna a ranar fushinsa.
Il Signore è alla tua destra, annienterà i re nel giorno della sua ira.
6 Zai hukunta al’ummai, yana tarawa gawawwaki yana kuma murƙushe masu mulkin dukan duniya.
Giudicherà i popoli: in mezzo a cadaveri ne stritolerà la testa su vasta terra.
7 Zai sha daga rafin da yake kusa da hanya; saboda haka zai ɗaga kansa sama.
Lungo il cammino si disseta al torrente e solleva alta la testa.

< Zabura 110 >