< Zabura 110 >

1 Ta Dawuda. Zabura ce. Ubangiji ya ce wa Ubangijina, “Zauna a hannun damana, sai na sa abokan gābanka su zama matashin sawunka.”
לדוד מזמור נאם יהוה לאדני שב לימיני עד אשית איביך הדם לרגליך׃
2 Ubangiji zai fadada ikon sandan mulkinka daga Sihiyona za ka yi mulki a tsakiyar abokan gābanka.
מטה עזך ישלח יהוה מציון רדה בקרב איביך׃
3 Rundunarka za su so yin yaƙi a ranarka ta yaƙi. Saye cikin ɗaukaka mai tsarki, daga cikin ciki na safiya za ka karɓi raɓar ƙuruciyarka.
עמך נדבת ביום חילך בהדרי קדש מרחם משחר לך טל ילדתיך׃
4 Ubangiji ya rantse ba zai kuma canja zuciyarsa ba, “Kai firist ne har abada, bisa ga tsarin Melkizedek.”
נשבע יהוה ולא ינחם אתה כהן לעולם על דברתי מלכי צדק׃
5 Ubangiji yana a hannun damanka; zai murƙushe sarakuna a ranar fushinsa.
אדני על ימינך מחץ ביום אפו מלכים׃
6 Zai hukunta al’ummai, yana tarawa gawawwaki yana kuma murƙushe masu mulkin dukan duniya.
ידין בגוים מלא גויות מחץ ראש על ארץ רבה׃
7 Zai sha daga rafin da yake kusa da hanya; saboda haka zai ɗaga kansa sama.
מנחל בדרך ישתה על כן ירים ראש׃

< Zabura 110 >