< Zabura 110 >

1 Ta Dawuda. Zabura ce. Ubangiji ya ce wa Ubangijina, “Zauna a hannun damana, sai na sa abokan gābanka su zama matashin sawunka.”
Psaume de David. L'Eternel a dit à mon Seigneur: assieds-toi à ma droite, jusqu’à ce que j'aie mis tes ennemis pour le marchepied de tes pieds.
2 Ubangiji zai fadada ikon sandan mulkinka daga Sihiyona za ka yi mulki a tsakiyar abokan gābanka.
L'Eternel transmettra de Sion le sceptre de ta force, [en disant]: Domine au milieu de tes ennemis.
3 Rundunarka za su so yin yaƙi a ranarka ta yaƙi. Saye cikin ɗaukaka mai tsarki, daga cikin ciki na safiya za ka karɓi raɓar ƙuruciyarka.
Ton peuple [sera un peuple plein] de franche volonté au jour [que tu assembleras] ton armée en sainte pompe; la rosée de ta jeunesse te [sera produite] du sein de l'aube du jour.
4 Ubangiji ya rantse ba zai kuma canja zuciyarsa ba, “Kai firist ne har abada, bisa ga tsarin Melkizedek.”
L'Eternel l'a juré, et il ne s'en repentira point, que tu es Sacrificateur éternellement, à la façon de Melchisédec.
5 Ubangiji yana a hannun damanka; zai murƙushe sarakuna a ranar fushinsa.
Le Seigneur est à ta droite, il froissera les Rois au jour de sa colère.
6 Zai hukunta al’ummai, yana tarawa gawawwaki yana kuma murƙushe masu mulkin dukan duniya.
Il exercera jugement sur les nations, il remplira tout de corps morts; il froissera le Chef [qui domine] sur un grand pays.
7 Zai sha daga rafin da yake kusa da hanya; saboda haka zai ɗaga kansa sama.
Il boira du torrent par le chemin, c'est pourquoi il lèvera haut la tête.

< Zabura 110 >