< Zabura 110 >

1 Ta Dawuda. Zabura ce. Ubangiji ya ce wa Ubangijina, “Zauna a hannun damana, sai na sa abokan gābanka su zama matashin sawunka.”
De David. Psaume. L’Eternel a dit à mon maître: "Assieds-toi à ma droite, jusqu’à ce que j’aie fait de tes ennemis un escabeau pour tes pieds."
2 Ubangiji zai fadada ikon sandan mulkinka daga Sihiyona za ka yi mulki a tsakiyar abokan gābanka.
L’Eternel étendra de Sion le sceptre de ta puissance: domine au milieu de tes ennemis.
3 Rundunarka za su so yin yaƙi a ranarka ta yaƙi. Saye cikin ɗaukaka mai tsarki, daga cikin ciki na safiya za ka karɓi raɓar ƙuruciyarka.
Ton peuple se montre plein de dévouement, le jour où tu déploies tes forces dans un saint appareil. Du sein de l’aurore t’arrive la rosée qui vivifie ta jeunesse.
4 Ubangiji ya rantse ba zai kuma canja zuciyarsa ba, “Kai firist ne har abada, bisa ga tsarin Melkizedek.”
L’Eternel en a fait le serment qu’il ne révoquera point: "Tu es prêtre pour l’éternité à la façon de Melchisédech."
5 Ubangiji yana a hannun damanka; zai murƙushe sarakuna a ranar fushinsa.
Le Seigneur est à ta droite, au jour de sa colère il brise des rois.
6 Zai hukunta al’ummai, yana tarawa gawawwaki yana kuma murƙushe masu mulkin dukan duniya.
Parmi les peuples il exerce la justice, accumule les cadavres; sur une étendue immense il fracasse des têtes.
7 Zai sha daga rafin da yake kusa da hanya; saboda haka zai ɗaga kansa sama.
Il boira sur la route de l’eau du torrent: aussi portera-t-il haut la tête.

< Zabura 110 >