< Zabura 110 >

1 Ta Dawuda. Zabura ce. Ubangiji ya ce wa Ubangijina, “Zauna a hannun damana, sai na sa abokan gābanka su zama matashin sawunka.”
Yahweh said to my lord [the king], “Sit [here], close to me, in the place of highest honor [MTY] until I [completely defeat] your enemies [MET] [and] make [them like] a stool for your feet!”
2 Ubangiji zai fadada ikon sandan mulkinka daga Sihiyona za ka yi mulki a tsakiyar abokan gābanka.
Yahweh [also said to him], “I will extend your power as king from Jerusalem [to other lands]; you will rule over all your enemies.
3 Rundunarka za su so yin yaƙi a ranarka ta yaƙi. Saye cikin ɗaukaka mai tsarki, daga cikin ciki na safiya za ka karɓi raɓar ƙuruciyarka.
On the day that you lead your armies into battle, many of your people will volunteer [to join your army]. Like the dew refreshes the earth early in the morning, young men will [encourage you by] coming to help you.”
4 Ubangiji ya rantse ba zai kuma canja zuciyarsa ba, “Kai firist ne har abada, bisa ga tsarin Melkizedek.”
Yahweh has made a solemn promise, and he will never change his mind; he has said to the king, “You will be a priest forever [serving Yahweh] like Melchizedek did.”
5 Ubangiji yana a hannun damanka; zai murƙushe sarakuna a ranar fushinsa.
Yahweh stands [in the place of highest honor] your right side; when he becomes angry, he will defeat [many kings].
6 Zai hukunta al’ummai, yana tarawa gawawwaki yana kuma murƙushe masu mulkin dukan duniya.
He will judge and punish the people of [many] nations; he will fill the land with their corpses. He will crush the heads of other kings all over the earth.
7 Zai sha daga rafin da yake kusa da hanya; saboda haka zai ɗaga kansa sama.
But my lord the king will drink from streams near the road; he will be refreshed after defeating his enemies.

< Zabura 110 >