< Zabura 110 >

1 Ta Dawuda. Zabura ce. Ubangiji ya ce wa Ubangijina, “Zauna a hannun damana, sai na sa abokan gābanka su zama matashin sawunka.”
Of David, a psalm. This said the Lord concerning my lord, “Sit at my right hand, till I set your foot on the neck of your foes.”
2 Ubangiji zai fadada ikon sandan mulkinka daga Sihiyona za ka yi mulki a tsakiyar abokan gābanka.
On Zion the Lord is wielding your sceptre of might, and charges you to rule over the foes that surround you.
3 Rundunarka za su so yin yaƙi a ranarka ta yaƙi. Saye cikin ɗaukaka mai tsarki, daga cikin ciki na safiya za ka karɓi raɓar ƙuruciyarka.
The day that you march to battle your people will follow you gladly young warriors in holy array, like dew-drops, born of the morning.
4 Ubangiji ya rantse ba zai kuma canja zuciyarsa ba, “Kai firist ne har abada, bisa ga tsarin Melkizedek.”
The Lord has sworn and will not repent, “As for you, you are priest for ever as Melchizedek was.”
5 Ubangiji yana a hannun damanka; zai murƙushe sarakuna a ranar fushinsa.
By your side will the Lord shatter kings on the day of his wrath.
6 Zai hukunta al’ummai, yana tarawa gawawwaki yana kuma murƙushe masu mulkin dukan duniya.
He will execute judgment filling the valleys with dead, the broad fields with shattered heads.
7 Zai sha daga rafin da yake kusa da hanya; saboda haka zai ɗaga kansa sama.
He will drink of the brook by the way, and march onward with uplifted head.

< Zabura 110 >