< Zabura 110 >
1 Ta Dawuda. Zabura ce. Ubangiji ya ce wa Ubangijina, “Zauna a hannun damana, sai na sa abokan gābanka su zama matashin sawunka.”
The LORD said to my Lord, Sit you at my right hand, until I make your enemies your footstool.
2 Ubangiji zai fadada ikon sandan mulkinka daga Sihiyona za ka yi mulki a tsakiyar abokan gābanka.
The LORD shall send the rod of your strength out of Zion: rule you in the middle of your enemies.
3 Rundunarka za su so yin yaƙi a ranarka ta yaƙi. Saye cikin ɗaukaka mai tsarki, daga cikin ciki na safiya za ka karɓi raɓar ƙuruciyarka.
Your people shall be willing in the day of your power, in the beauties of holiness from the womb of the morning: you have the dew of your youth.
4 Ubangiji ya rantse ba zai kuma canja zuciyarsa ba, “Kai firist ne har abada, bisa ga tsarin Melkizedek.”
The LORD has sworn, and will not repent, You are a priest for ever after the order of Melchizedek.
5 Ubangiji yana a hannun damanka; zai murƙushe sarakuna a ranar fushinsa.
The Lord at your right hand shall strike through kings in the day of his wrath.
6 Zai hukunta al’ummai, yana tarawa gawawwaki yana kuma murƙushe masu mulkin dukan duniya.
He shall judge among the heathen, he shall fill the places with the dead bodies; he shall wound the heads over many countries.
7 Zai sha daga rafin da yake kusa da hanya; saboda haka zai ɗaga kansa sama.
He shall drink of the brook in the way: therefore shall he lift up the head.