< Zabura 110 >

1 Ta Dawuda. Zabura ce. Ubangiji ya ce wa Ubangijina, “Zauna a hannun damana, sai na sa abokan gābanka su zama matashin sawunka.”
A Psalme of David. The Lord said vnto my Lord, Sit thou at my right hand, vntill I make thine enemies thy footestoole.
2 Ubangiji zai fadada ikon sandan mulkinka daga Sihiyona za ka yi mulki a tsakiyar abokan gābanka.
The Lord shall send the rod of thy power out of Zion: be thou ruler in the middes of thine enemies.
3 Rundunarka za su so yin yaƙi a ranarka ta yaƙi. Saye cikin ɗaukaka mai tsarki, daga cikin ciki na safiya za ka karɓi raɓar ƙuruciyarka.
Thy people shall come willingly at the time of assembling thine armie in holy beautie: the youth of thy wombe shalbe as the morning dewe.
4 Ubangiji ya rantse ba zai kuma canja zuciyarsa ba, “Kai firist ne har abada, bisa ga tsarin Melkizedek.”
The Lord sware and wil not repent, Thou art a Priest for euer after ye order of Melchi-zedek.
5 Ubangiji yana a hannun damanka; zai murƙushe sarakuna a ranar fushinsa.
The Lord, that is at thy right hand, shall wound Kings in the day of his wrath.
6 Zai hukunta al’ummai, yana tarawa gawawwaki yana kuma murƙushe masu mulkin dukan duniya.
He shalbe iudge among the heathen: he shall fill all with dead bodies, and smite the head ouer great countreis.
7 Zai sha daga rafin da yake kusa da hanya; saboda haka zai ɗaga kansa sama.
He shall drinke of the brooke in the way: therefore shall he lift vp his head.

< Zabura 110 >