< Zabura 110 >

1 Ta Dawuda. Zabura ce. Ubangiji ya ce wa Ubangijina, “Zauna a hannun damana, sai na sa abokan gābanka su zama matashin sawunka.”
Psalm of David. Jehovah said unto my Lord, Sit at my right hand, until I put thine enemies [as] footstool of thy feet.
2 Ubangiji zai fadada ikon sandan mulkinka daga Sihiyona za ka yi mulki a tsakiyar abokan gābanka.
Jehovah shall send the sceptre of thy might out of Zion: rule in the midst of thine enemies.
3 Rundunarka za su so yin yaƙi a ranarka ta yaƙi. Saye cikin ɗaukaka mai tsarki, daga cikin ciki na safiya za ka karɓi raɓar ƙuruciyarka.
Thy people shall be willing in the day of thy power, in holy splendour: from the womb of the morning [shall come] to thee the dew of thy youth.
4 Ubangiji ya rantse ba zai kuma canja zuciyarsa ba, “Kai firist ne har abada, bisa ga tsarin Melkizedek.”
Jehovah hath sworn, and will not repent, Thou art priest for ever after the order of Melchisedek.
5 Ubangiji yana a hannun damanka; zai murƙushe sarakuna a ranar fushinsa.
The Lord at thy right hand will smite through kings in the day of his anger.
6 Zai hukunta al’ummai, yana tarawa gawawwaki yana kuma murƙushe masu mulkin dukan duniya.
He shall judge among the nations; he shall fill [all places] with dead bodies; he shall smite through the head over a great country.
7 Zai sha daga rafin da yake kusa da hanya; saboda haka zai ɗaga kansa sama.
He shall drink of the brook in the way; therefore shall he lift up the head.

< Zabura 110 >