< Zabura 11 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Don busa. Ta Dawuda. A wurin Ubangiji ne nake samun mafaka. Yaya za ku ce mini, “Ka yi firiya kamar tsuntsu zuwa duwatsu.
in finem psalmus David in Domino confido quomodo dicitis animae meae transmigra in montes sicut passer
2 Gama duba, mugaye sun tanƙware bakkunansu; sun kuma ɗana kibiyoyinsu don su harbi mutanen kirki a zuciya daga cikin duhu.
quoniam ecce peccatores intenderunt arcum paraverunt sagittas suas in faretra ut sagittent in obscuro rectos corde
3 Sa’ad da aka tumɓuke tushe, me adali zai iya yi?”
quoniam quae perfecisti destruxerunt iustus autem quid fecit
4 Ubangiji yana cikin haikalinsa mai tsarki; Ubangiji yana a kursiyinsa a sama. Yana kallon’ya’yan mutane; idanunsa suna bincike su.
Dominus in templo sancto suo Dominus in caelo sedis eius oculi eius in pauperem respiciunt palpebrae eius interrogant filios hominum
5 Ubangiji yana bincike adalai, amma ransa yana ƙi mugaye da masu son rikici.
Dominus interrogat iustum et impium qui autem diligit iniquitatem odit animam suam
6 A kan mugaye zai zuba garwashin wuta mai zafi da kuma kibiritu; iska mai zafi zai zama rabonsu.
pluet super peccatores laqueos ignis et sulphur et spiritus procellarum pars calicis eorum
7 Gama Ubangiji mai adalci ne, yana ƙaunar gaskiya masu adalci za su ga fuskarsa.
quoniam iustus Dominus et iustitias dilexit aequitatem vidit vultus eius