< Zabura 11 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Don busa. Ta Dawuda. A wurin Ubangiji ne nake samun mafaka. Yaya za ku ce mini, “Ka yi firiya kamar tsuntsu zuwa duwatsu.
“To the chief musician, by David.” In the Lord have I put my trust: how can ye say to my soul, Flee to your mountain as a bird?
2 Gama duba, mugaye sun tanƙware bakkunansu; sun kuma ɗana kibiyoyinsu don su harbi mutanen kirki a zuciya daga cikin duhu.
For lo, the wicked bend their bow, they arrange their arrow upon the string, to shoot in the dark at the upright in heart.
3 Sa’ad da aka tumɓuke tushe, me adali zai iya yi?”
For [if] the foundations be torn down, what can the righteous do?
4 Ubangiji yana cikin haikalinsa mai tsarki; Ubangiji yana a kursiyinsa a sama. Yana kallon’ya’yan mutane; idanunsa suna bincike su.
The Lord is in his holy temple, the Lord hath his throne in the heavens, his eyes behold, his eyelids prove, the children of men.
5 Ubangiji yana bincike adalai, amma ransa yana ƙi mugaye da masu son rikici.
The Lord proveth the righteous; but the wicked and him that loveth violence his soul hateth.
6 A kan mugaye zai zuba garwashin wuta mai zafi da kuma kibiritu; iska mai zafi zai zama rabonsu.
He letteth rain upon the wicked burning coals, fire and brimstone; and a glowing wind is the portion of their cup.
7 Gama Ubangiji mai adalci ne, yana ƙaunar gaskiya masu adalci za su ga fuskarsa.
For righteous is the Lord, he loveth righteousness: his countenance doth behold the upright.