< Zabura 11 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Don busa. Ta Dawuda. A wurin Ubangiji ne nake samun mafaka. Yaya za ku ce mini, “Ka yi firiya kamar tsuntsu zuwa duwatsu.
Unto the end. A psalm for David. In the Lord I put my trust: how then do you say to my soul: Get thee away from hence to the mountain like a sparrow?
2 Gama duba, mugaye sun tanƙware bakkunansu; sun kuma ɗana kibiyoyinsu don su harbi mutanen kirki a zuciya daga cikin duhu.
For, lo, the wicked have bent their bow; they have prepared their arrows in the quiver; to shoot in the dark the upright of heart.
3 Sa’ad da aka tumɓuke tushe, me adali zai iya yi?”
For they have destroyed the things which thou hast made: but what has the just man done?
4 Ubangiji yana cikin haikalinsa mai tsarki; Ubangiji yana a kursiyinsa a sama. Yana kallon’ya’yan mutane; idanunsa suna bincike su.
The Lord is in his holy temple, the Lord’s throne is in heaven. His eyes look on the poor man: his eyelids examine the sons of men.
5 Ubangiji yana bincike adalai, amma ransa yana ƙi mugaye da masu son rikici.
The Lord trieth the just and the wicked: but he that loveth iniquity hateth his own soul.
6 A kan mugaye zai zuba garwashin wuta mai zafi da kuma kibiritu; iska mai zafi zai zama rabonsu.
He shall rain snares upon sinners: fire and brimstone and storms of winds shall be the portion of their cup.
7 Gama Ubangiji mai adalci ne, yana ƙaunar gaskiya masu adalci za su ga fuskarsa.
For the Lord is just, and hath loved justice: his countenance hath beheld righteousness.