< Zabura 11 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Don busa. Ta Dawuda. A wurin Ubangiji ne nake samun mafaka. Yaya za ku ce mini, “Ka yi firiya kamar tsuntsu zuwa duwatsu.
To the chief Musician. [A Psalm] of David. In Jehovah have I put my trust: how say ye to my soul, Flee [as] a bird to your mountain?
2 Gama duba, mugaye sun tanƙware bakkunansu; sun kuma ɗana kibiyoyinsu don su harbi mutanen kirki a zuciya daga cikin duhu.
For behold, the wicked bend the bow, they make ready their arrow upon the string, that they may in darkness shoot at the upright in heart.
3 Sa’ad da aka tumɓuke tushe, me adali zai iya yi?”
If the foundations be destroyed, what shall the righteous do?
4 Ubangiji yana cikin haikalinsa mai tsarki; Ubangiji yana a kursiyinsa a sama. Yana kallon’ya’yan mutane; idanunsa suna bincike su.
Jehovah [is] in the temple of his holiness; Jehovah, — his throne is in the heavens: his eyes behold, his eyelids try the children of men.
5 Ubangiji yana bincike adalai, amma ransa yana ƙi mugaye da masu son rikici.
Jehovah trieth the righteous one; but the wicked, and him that loveth violence, his soul hateth.
6 A kan mugaye zai zuba garwashin wuta mai zafi da kuma kibiritu; iska mai zafi zai zama rabonsu.
Upon the wicked he shall rain snares, fire and brimstone; and scorching wind shall be the portion of their cup.
7 Gama Ubangiji mai adalci ne, yana ƙaunar gaskiya masu adalci za su ga fuskarsa.
For righteous is Jehovah; he loveth righteousness, his countenance doth behold the upright.

< Zabura 11 >