< Zabura 11 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Don busa. Ta Dawuda. A wurin Ubangiji ne nake samun mafaka. Yaya za ku ce mini, “Ka yi firiya kamar tsuntsu zuwa duwatsu.
For the choirmaster. Of David. In the LORD I take refuge. How then can you say to me: “Flee like a bird to your mountain!
2 Gama duba, mugaye sun tanƙware bakkunansu; sun kuma ɗana kibiyoyinsu don su harbi mutanen kirki a zuciya daga cikin duhu.
For behold, the wicked bend their bows. They set their arrow on the string to shoot from the shadows at the upright in heart.
3 Sa’ad da aka tumɓuke tushe, me adali zai iya yi?”
If the foundations are destroyed, what can the righteous do?”
4 Ubangiji yana cikin haikalinsa mai tsarki; Ubangiji yana a kursiyinsa a sama. Yana kallon’ya’yan mutane; idanunsa suna bincike su.
The LORD is in His holy temple; the LORD is on His heavenly throne. His eyes are watching closely; they examine the sons of men.
5 Ubangiji yana bincike adalai, amma ransa yana ƙi mugaye da masu son rikici.
The LORD tests the righteous and the wicked; His soul hates the lover of violence.
6 A kan mugaye zai zuba garwashin wuta mai zafi da kuma kibiritu; iska mai zafi zai zama rabonsu.
On the wicked He will rain down fiery coals and sulfur; a scorching wind will be their portion.
7 Gama Ubangiji mai adalci ne, yana ƙaunar gaskiya masu adalci za su ga fuskarsa.
For the LORD is righteous; He loves justice. The upright will see His face.

< Zabura 11 >