< Zabura 109 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda. Zabura ce. Ya Allah, wanda nake yabo, kada ka yi shiru,
Müzik şefi için - Davut'un mezmuru Ey övgüler sunduğum Tanrı, Sessiz kalma!
2 gama mugaye da masu ruɗu sun buɗe bakunansu a kaina; sun yi magana a kaina da harsunan ƙarya.
Çünkü kötüler, yalancılar Bana karşı ağzını açtı, Karalıyorlar beni.
3 Da kalmomin ƙiyayya sun kewaye ni; sun tasar mini ba dalili.
Nefret dolu sözlerle beni kuşatıp Yok yere bana savaş açtılar.
4 A maimakon ƙauna sun sāka mini da zargi, amma ni mutum ne mai addu’a.
Sevgime karşılık bana düşman oldular, Bense dua etmekteyim.
5 Sun sāka mini alheri da mugunta, ƙauna kuma da ƙiyayya.
İyiliğime kötülük, Sevgime nefretle karşılık verdiler.
6 Ka naɗa mugun mutum yă yi hamayya da shi; bari mai zargi yă tsaya a hannun damansa.
Kötü bir adam koy düşmanın başına, Sağında onu suçlayan biri dursun!
7 Sa’ad da aka yi masa shari’a, bari a same shi da laifi, bari kuma addu’o’insa su hukunta shi.
Yargılanınca suçlu çıksın, Duası bile günah sayılsın!
8 Bari kwanakinsa su zama kaɗan; bari wani yă ɗauki wurinsa na shugabanci.
Ömrü kısa olsun, Görevini bir başkası üstlensin!
9 Bari’ya’yansa su zama marayu matarsa kuma gwauruwa.
Çocukları öksüz, Karısı dul kalsın!
10 Bari’ya’yansa su zama masu yawo suna bara; bari a yi ta koransu daga gidajensu da suke kufai.
Çocukları avare gezip dilensin, Yıkık evlerinden uzakta yiyecek arasın!
11 Bari mai binsa bashi yă ƙwace dukan abin da yake da shi; bari baƙi su washe amfanin aikinsa.
Bütün malları tefecinin ağına düşsün, Emeğini yabancılar yağmalasın!
12 Bari kada kowa yă yi masa alheri ko yă ji tausayin marayunsa.
Kimse ona sevgi göstermesin, Öksüzlerine acıyan olmasın!
13 Bari duk zuriyarsa su mutu, a shafe sunayensu daga tsara mai zuwa.
Soyu kurusun, Bir kuşak sonra adı silinsin!
14 Bari a tuna da laifin kakanninsa a gaban Ubangiji; bari kada a taɓa shafe zunubin mahaifiyarsa.
Atalarının suçları RAB'bin önünde anılsın, Annesinin günahı silinmesin!
15 Bari zunubansu su kasance a gaban Ubangiji kullum, don yă sa a manta da su daga duniya.
Günahları hep RAB'bin önünde dursun, RAB anılarını yok etsin yeryüzünden!
16 Gama bai taɓa yin tunanin yin alheri ba, amma ya tsananta wa matalauta da mabukata da kuma masu fid da zuciya har suka mutu.
Çünkü düşmanım sevgi göstermeyi düşünmedi, Ölesiye baskı yaptı mazluma, yoksula, Yüreği kırık insana.
17 Yana jin daɗin la’antarwa, bari yă dawo a kansa; ba ya son sa albarka, bari kada kowa yă sa masa albarka.
Sevdiği lanet başına gelsin! Madem kutsamaktan hoşlanmıyor, Uzak olsun ondan kutsamak!
18 Ya sa la’antarwa kamar rigarsa; ta shiga cikin jikinsa kamar ruwa, cikin ƙasusuwansa kamar mai.
Laneti bir giysi gibi giydi, Su gibi içine, yağ gibi kemiklerine işlesin lanet!
19 Bari tă zama kamar mayafin da aka ɗaura kewaye da shi, kamar ɗamara da aka ɗaura kewaye da shi har abada.
Bir giysi gibi onu örtünsün, Bir kuşak gibi hep onu sarsın!
20 Bari wannan yă zama sakayyar Ubangiji ga masu zargina, ga waɗanda suke mugayen maganganu a kaina.
Düşmanlarıma, beni kötüleyenlere, RAB böyle karşılık versin!
21 Amma kai, ya Ubangiji Mai Iko Duka, ka yi da ni da kyau saboda sunanka; ta alherin ƙaunarka, ka cece ni.
Ama sen, ey Egemen RAB, Adın uğruna bana ilgi göster; Kurtar beni, iyiliğin, sevgin uğruna!
22 Gama ni matalauci ne mai bukata kuma, zuciyata kuwa ta yi rauni a cikina.
Çünkü düşkün ve yoksulum, Yüreğim yaralı içimde.
23 Na ɓace kamar inuwar yamma; ana kakkaɓe ni kamar fāra.
Batan güneş gibi geçip gidiyorum, Çekirge gibi silkilip atılıyorum.
24 Gwiwoyina suna mutuwa saboda azumi; jikina ya rame ba kuma ƙarfi.
Dizlerim titriyor oruç tutmaktan; Bir deri bir kemiğe döndüm.
25 Na zama abin dariya ga masu zargina; sa’ad da suka gan ni, suka kaɗa kawunansu.
Düşmanlarıma yüzkarası oldum; Beni görünce kafalarını sallıyorlar!
26 Ka taimake ni, ya Ubangiji Allahna; ka cece ni bisa ga ƙaunarka.
Yardım et bana, ya RAB Tanrım; Kurtar beni sevgin uğruna!
27 Bari su san cewa hannunka ne, cewa kai ne, ya Ubangiji, ka yi shi.
Bilsinler bu işte senin elin olduğunu, Bunu senin yaptığını, ya RAB!
28 Za su iya la’anta, amma kai za ka sa albarka; sa’ad da suka tasar za su sha kunya, amma bawanka zai yi farin ciki.
Varsın lanet etsin onlar, sen kutsa beni, Bana saldıranlar utanacak, Ben kulunsa sevineceğim.
29 Masu zargina za su sha kunya za a rufe su da kunya kamar mayafi.
Rezilliğe bürünsün beni suçlayanlar, Kaftan giyer gibi utançlarıyla örtünsünler!
30 Da bakina zan ɗaukaka Ubangiji sosai; cikin babban taro zan yabe shi.
RAB'be çok şükredeceğim, Kalabalığın arasında O'na övgüler dizeceğim;
31 Gama yana tsaya a hannun damar mai bukata, don yă cece ransa daga waɗanda suke hukunta shi.
Çünkü O yoksulun sağında durur, Onu yargılayanlardan kurtarmak için.