< Zabura 109 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda. Zabura ce. Ya Allah, wanda nake yabo, kada ka yi shiru,
¡O Dios de mi alabanza! no calles:
2 gama mugaye da masu ruɗu sun buɗe bakunansu a kaina; sun yi magana a kaina da harsunan ƙarya.
Porque boca de impío, y boca de engañador se han abierto sobre mí: han hablado de mí con lengua mentirosa.
3 Da kalmomin ƙiyayya sun kewaye ni; sun tasar mini ba dalili.
Y con palabras de odio me rodearon; y pelearon contra mí sin causa.
4 A maimakon ƙauna sun sāka mini da zargi, amma ni mutum ne mai addu’a.
En pago de mi amor me han sido adversarios; y yo, hacía oración.
5 Sun sāka mini alheri da mugunta, ƙauna kuma da ƙiyayya.
Y pusieron contra mí mal por bien; y odio por mi amor.
6 Ka naɗa mugun mutum yă yi hamayya da shi; bari mai zargi yă tsaya a hannun damansa.
Pon sobre él al impío, y Satanás esté a su diestra.
7 Sa’ad da aka yi masa shari’a, bari a same shi da laifi, bari kuma addu’o’insa su hukunta shi.
Cuando fuere juzgado, salga por impío, y su oración sea para pecado.
8 Bari kwanakinsa su zama kaɗan; bari wani yă ɗauki wurinsa na shugabanci.
Sean sus días pocos: tome otro su oficio.
9 Bari’ya’yansa su zama marayu matarsa kuma gwauruwa.
Sean sus hijos huérfanos; y su mujer viuda.
10 Bari’ya’yansa su zama masu yawo suna bara; bari a yi ta koransu daga gidajensu da suke kufai.
Y anden sus hijos vagabundos, y mendiguen; y procuren de sus desiertos.
11 Bari mai binsa bashi yă ƙwace dukan abin da yake da shi; bari baƙi su washe amfanin aikinsa.
Enrede el acreedor todo lo que tiene; y extraños saqueen su trabajo.
12 Bari kada kowa yă yi masa alheri ko yă ji tausayin marayunsa.
No tenga quien le haga misericordia; ni haya quien tenga compasión de sus huérfanos.
13 Bari duk zuriyarsa su mutu, a shafe sunayensu daga tsara mai zuwa.
Su posteridad sea talada: en segunda generación sea raído su nombre.
14 Bari a tuna da laifin kakanninsa a gaban Ubangiji; bari kada a taɓa shafe zunubin mahaifiyarsa.
Venga en memoria cerca de Jehová la maldad de sus padres; y el pecado de su madre no sea raído.
15 Bari zunubansu su kasance a gaban Ubangiji kullum, don yă sa a manta da su daga duniya.
Estén delante de Jehová siempre; y él corte de la tierra su memoria.
16 Gama bai taɓa yin tunanin yin alheri ba, amma ya tsananta wa matalauta da mabukata da kuma masu fid da zuciya har suka mutu.
Por cuanto no se acordó de hacer misericordia; y persiguió al varón afligido, y menesteroso, y quebrantado de corazón, para matarle.
17 Yana jin daɗin la’antarwa, bari yă dawo a kansa; ba ya son sa albarka, bari kada kowa yă sa masa albarka.
Y amó la maldición, y vínole; y no quiso la bendición, y ella se alejó de él.
18 Ya sa la’antarwa kamar rigarsa; ta shiga cikin jikinsa kamar ruwa, cikin ƙasusuwansa kamar mai.
Y vistióse de maldición como de su vestido; y entró como agua en sus entrañas, y como aceite en sus huesos.
19 Bari tă zama kamar mayafin da aka ɗaura kewaye da shi, kamar ɗamara da aka ɗaura kewaye da shi har abada.
Séale como vestido con que se cubra; y en lugar de cinto con que siempre se ciña.
20 Bari wannan yă zama sakayyar Ubangiji ga masu zargina, ga waɗanda suke mugayen maganganu a kaina.
Este sea el salario, de parte de Jehová, de los que me calumnían; y los que hablan mal contra mi alma.
21 Amma kai, ya Ubangiji Mai Iko Duka, ka yi da ni da kyau saboda sunanka; ta alherin ƙaunarka, ka cece ni.
Y tú, Jehová Señor, haz conmigo por causa de tu nombre: escápame, porque tu misericordia es buena.
22 Gama ni matalauci ne mai bukata kuma, zuciyata kuwa ta yi rauni a cikina.
Porque yo soy afligido y necesitado; y mi corazón está herido dentro de mí.
23 Na ɓace kamar inuwar yamma; ana kakkaɓe ni kamar fāra.
Como la sombra cuando declina me voy; soy sacudido como langosta.
24 Gwiwoyina suna mutuwa saboda azumi; jikina ya rame ba kuma ƙarfi.
Mis rodillas están enflaquecidas a causa del ayuno; y mi carne está falta de gordura.
25 Na zama abin dariya ga masu zargina; sa’ad da suka gan ni, suka kaɗa kawunansu.
Yo he sido a ellos oprobio: mirábanme, y meneaban su cabeza.
26 Ka taimake ni, ya Ubangiji Allahna; ka cece ni bisa ga ƙaunarka.
Ayúdame, Jehová Dios mío: sálvame conforme a tu misericordia;
27 Bari su san cewa hannunka ne, cewa kai ne, ya Ubangiji, ka yi shi.
Y entiendan que esta es tu mano; que tú, Jehová, has hecho esto.
28 Za su iya la’anta, amma kai za ka sa albarka; sa’ad da suka tasar za su sha kunya, amma bawanka zai yi farin ciki.
Maldigan ellos, y bendigas tú; levántense, mas sean avergonzados: y tu siervo sea alegrado.
29 Masu zargina za su sha kunya za a rufe su da kunya kamar mayafi.
Sean vestidos de vergüenza los que me calumnían; y sean cubiertos como de manto de su confusión.
30 Da bakina zan ɗaukaka Ubangiji sosai; cikin babban taro zan yabe shi.
Yo alabaré a Jehová en gran manera con mi boca; y en medio de muchos le loaré:
31 Gama yana tsaya a hannun damar mai bukata, don yă cece ransa daga waɗanda suke hukunta shi.
Porque él se pondrá a la diestra del pobre; para librar su alma de los que juzgan.