< Zabura 109 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda. Zabura ce. Ya Allah, wanda nake yabo, kada ka yi shiru,
Боже, хвалы моея не премолчи:
2 gama mugaye da masu ruɗu sun buɗe bakunansu a kaina; sun yi magana a kaina da harsunan ƙarya.
яко уста грешнича и уста льстиваго на мя отверзошася, глаголаша на мя языком льстивым,
3 Da kalmomin ƙiyayya sun kewaye ni; sun tasar mini ba dalili.
и словесы ненавистными обыдоша мя, и брашася со мною туне.
4 A maimakon ƙauna sun sāka mini da zargi, amma ni mutum ne mai addu’a.
Вместо еже любити мя, оболгаху мя, аз же моляхся:
5 Sun sāka mini alheri da mugunta, ƙauna kuma da ƙiyayya.
и положиша на мя злая за благая, и ненависть за возлюбление мое.
6 Ka naɗa mugun mutum yă yi hamayya da shi; bari mai zargi yă tsaya a hannun damansa.
Постави на него грешника, и диавол да станет одесную его:
7 Sa’ad da aka yi masa shari’a, bari a same shi da laifi, bari kuma addu’o’insa su hukunta shi.
внегда судитися ему, да изыдет осужден, и молитва его да будет в грех.
8 Bari kwanakinsa su zama kaɗan; bari wani yă ɗauki wurinsa na shugabanci.
Да будут дние его мали, и епископство его да приимет ин:
9 Bari’ya’yansa su zama marayu matarsa kuma gwauruwa.
да будут сынове его сири, и жена его вдова:
10 Bari’ya’yansa su zama masu yawo suna bara; bari a yi ta koransu daga gidajensu da suke kufai.
движущеся да преселятся сынове его и воспросят, да изгнани будут из домов своих.
11 Bari mai binsa bashi yă ƙwace dukan abin da yake da shi; bari baƙi su washe amfanin aikinsa.
Да взыщет заимодавец вся, елика суть его: и да восхитят чуждии труды его.
12 Bari kada kowa yă yi masa alheri ko yă ji tausayin marayunsa.
Да не будет ему заступника, ниже да будет ущедряяй сироты его:
13 Bari duk zuriyarsa su mutu, a shafe sunayensu daga tsara mai zuwa.
да будут чада его в погубление, в роде единем да потребится имя его.
14 Bari a tuna da laifin kakanninsa a gaban Ubangiji; bari kada a taɓa shafe zunubin mahaifiyarsa.
Да воспомянется беззаконие отец его пред Господем, и грех матере его да не очистится:
15 Bari zunubansu su kasance a gaban Ubangiji kullum, don yă sa a manta da su daga duniya.
да будут пред Господем выну, и да потребится от земли память их:
16 Gama bai taɓa yin tunanin yin alheri ba, amma ya tsananta wa matalauta da mabukata da kuma masu fid da zuciya har suka mutu.
занеже не помяну сотворити милость, и погна человека нища и убога, и умилена сердцем умертвити.
17 Yana jin daɗin la’antarwa, bari yă dawo a kansa; ba ya son sa albarka, bari kada kowa yă sa masa albarka.
И возлюби клятву, и приидет ему: и не восхоте благословения, и удалится от него.
18 Ya sa la’antarwa kamar rigarsa; ta shiga cikin jikinsa kamar ruwa, cikin ƙasusuwansa kamar mai.
И облечеся в клятву яко в ризу, и вниде яко вода во утробу его и яко елей в кости его:
19 Bari tă zama kamar mayafin da aka ɗaura kewaye da shi, kamar ɗamara da aka ɗaura kewaye da shi har abada.
да будет ему яко риза, в нюже облачится, и яко пояс, имже выну опоясуется.
20 Bari wannan yă zama sakayyar Ubangiji ga masu zargina, ga waɗanda suke mugayen maganganu a kaina.
Сие дело оболгающих мя у Господа и глаголющих лукавая на душу мою.
21 Amma kai, ya Ubangiji Mai Iko Duka, ka yi da ni da kyau saboda sunanka; ta alherin ƙaunarka, ka cece ni.
И Ты, Господи, Господи, сотвори со мною имене ради Твоего, яко блага милость Твоя:
22 Gama ni matalauci ne mai bukata kuma, zuciyata kuwa ta yi rauni a cikina.
избави мя, яко нищь и убог есмь аз, и сердце мое смятеся внутрь мене.
23 Na ɓace kamar inuwar yamma; ana kakkaɓe ni kamar fāra.
Яко сень, внегда уклонитися ей, отяхся: стрясохся яко прузи.
24 Gwiwoyina suna mutuwa saboda azumi; jikina ya rame ba kuma ƙarfi.
Колена моя изнемогоста от поста, и плоть моя изменися елеа ради.
25 Na zama abin dariya ga masu zargina; sa’ad da suka gan ni, suka kaɗa kawunansu.
И аз бых поношение им: видеша мя, покиваша главами своими.
26 Ka taimake ni, ya Ubangiji Allahna; ka cece ni bisa ga ƙaunarka.
Помози ми, Господи Боже мой, и спаси мя по милости Твоей:
27 Bari su san cewa hannunka ne, cewa kai ne, ya Ubangiji, ka yi shi.
и да разумеют, яко рука Твоя сия, и Ты, Господи, сотворил еси ю.
28 Za su iya la’anta, amma kai za ka sa albarka; sa’ad da suka tasar za su sha kunya, amma bawanka zai yi farin ciki.
Прокленут тии, и Ты благословиши: востающии на мя да постыдятся, раб же Твой возвеселится.
29 Masu zargina za su sha kunya za a rufe su da kunya kamar mayafi.
Да облекутся оболгающии мя в срамоту и одеждутся яко одеждою студом своим.
30 Da bakina zan ɗaukaka Ubangiji sosai; cikin babban taro zan yabe shi.
Исповемся Господеви зело усты моими и посреде многих восхвалю Его:
31 Gama yana tsaya a hannun damar mai bukata, don yă cece ransa daga waɗanda suke hukunta shi.
яко преста одесную убогаго, еже спасти от гонящих душу мою.

< Zabura 109 >