< Zabura 109 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda. Zabura ce. Ya Allah, wanda nake yabo, kada ka yi shiru,
Para o músico chefe. Um Salmo de David. Deus do meu louvor, não fique calado,
2 gama mugaye da masu ruɗu sun buɗe bakunansu a kaina; sun yi magana a kaina da harsunan ƙarya.
pois eles abriram a boca dos ímpios e a boca do engano contra mim. Eles me falaram com uma língua mentirosa.
3 Da kalmomin ƙiyayya sun kewaye ni; sun tasar mini ba dalili.
Eles também me cercaram com palavras de ódio, e lutou contra mim sem uma causa.
4 A maimakon ƙauna sun sāka mini da zargi, amma ni mutum ne mai addu’a.
Em troca do meu amor, eles são meus adversários; mas eu estou em oração.
5 Sun sāka mini alheri da mugunta, ƙauna kuma da ƙiyayya.
Eles me recompensaram com o mal pelo bem, e ódio por meu amor.
6 Ka naɗa mugun mutum yă yi hamayya da shi; bari mai zargi yă tsaya a hannun damansa.
Colocar um homem malvado sobre ele. Deixe um adversário de pé à sua direita.
7 Sa’ad da aka yi masa shari’a, bari a same shi da laifi, bari kuma addu’o’insa su hukunta shi.
Quando ele for julgado, deixe-o sair culpado. Que sua oração seja transformada em pecado.
8 Bari kwanakinsa su zama kaɗan; bari wani yă ɗauki wurinsa na shugabanci.
Que seus dias sejam poucos. Deixe outro tomar seu cargo.
9 Bari’ya’yansa su zama marayu matarsa kuma gwauruwa.
Que seus filhos sejam órfãos de pai, e sua esposa uma viúva.
10 Bari’ya’yansa su zama masu yawo suna bara; bari a yi ta koransu daga gidajensu da suke kufai.
Let seus filhos andam vagueando mendigos. Que sejam procurados a partir de suas ruínas.
11 Bari mai binsa bashi yă ƙwace dukan abin da yake da shi; bari baƙi su washe amfanin aikinsa.
Let o credor apreende tudo o que tem. Deixe os estranhos saquearem o fruto de seu trabalho.
12 Bari kada kowa yă yi masa alheri ko yă ji tausayin marayunsa.
Que não haja ninguém para lhe estender a gentileza, nem que haja alguém que tenha piedade de seus filhos sem pai.
13 Bari duk zuriyarsa su mutu, a shafe sunayensu daga tsara mai zuwa.
Deixe sua posteridade ser cortada. Na geração seguinte, deixe seu nome ser apagado.
14 Bari a tuna da laifin kakanninsa a gaban Ubangiji; bari kada a taɓa shafe zunubin mahaifiyarsa.
Que a iniqüidade de seus pais seja lembrada por Javé. Não deixe que o pecado de sua mãe seja apagado.
15 Bari zunubansu su kasance a gaban Ubangiji kullum, don yă sa a manta da su daga duniya.
Deixe-os estar diante de Yahweh continuamente, que ele possa cortar a memória deles da terra;
16 Gama bai taɓa yin tunanin yin alheri ba, amma ya tsananta wa matalauta da mabukata da kuma masu fid da zuciya har suka mutu.
porque ele não se lembrava de mostrar gentileza, mas perseguiu os pobres e necessitados, os partidos de coração, para matá-los.
17 Yana jin daɗin la’antarwa, bari yă dawo a kansa; ba ya son sa albarka, bari kada kowa yă sa masa albarka.
Yes, ele adorava praguejar, e isso chegou até ele. Ele não se deliciou com a bênção, e isso estava longe dele.
18 Ya sa la’antarwa kamar rigarsa; ta shiga cikin jikinsa kamar ruwa, cikin ƙasusuwansa kamar mai.
Ele também se vestiu de maldição como com sua roupa. Entrou em suas partes internas como água, como óleo em seus ossos.
19 Bari tă zama kamar mayafin da aka ɗaura kewaye da shi, kamar ɗamara da aka ɗaura kewaye da shi har abada.
Que seja para ele como a roupa com a qual ele se cobre, para o cinto que está sempre ao seu redor.
20 Bari wannan yă zama sakayyar Ubangiji ga masu zargina, ga waɗanda suke mugayen maganganu a kaina.
Esta é a recompensa dos meus adversários de Yahweh, daqueles que falam mal contra a minha alma.
21 Amma kai, ya Ubangiji Mai Iko Duka, ka yi da ni da kyau saboda sunanka; ta alherin ƙaunarka, ka cece ni.
Mas lide comigo, Yahweh o Senhor, em nome de seu nome, porque sua bondade amorosa é boa, me entregue;
22 Gama ni matalauci ne mai bukata kuma, zuciyata kuwa ta yi rauni a cikina.
pois sou pobre e necessitado. Meu coração está ferido dentro de mim.
23 Na ɓace kamar inuwar yamma; ana kakkaɓe ni kamar fāra.
Desvaneco-me como uma sombra noturna. Sou sacudido como um gafanhoto.
24 Gwiwoyina suna mutuwa saboda azumi; jikina ya rame ba kuma ƙarfi.
Meus joelhos estão fracos por causa do jejum. Meu corpo é fino e carente de gordura.
25 Na zama abin dariya ga masu zargina; sa’ad da suka gan ni, suka kaɗa kawunansu.
Também me tornei uma reprovação para eles. Quando eles me vêem, abanam a cabeça.
26 Ka taimake ni, ya Ubangiji Allahna; ka cece ni bisa ga ƙaunarka.
Ajude-me, Yahweh, meu Deus. Salve-me de acordo com sua amorosa bondade;
27 Bari su san cewa hannunka ne, cewa kai ne, ya Ubangiji, ka yi shi.
para que eles saibam que esta é a sua mão; que você, Javé, o fez.
28 Za su iya la’anta, amma kai za ka sa albarka; sa’ad da suka tasar za su sha kunya, amma bawanka zai yi farin ciki.
Eles podem amaldiçoar, mas você abençoa. Quando eles surgirem, eles serão envergonhados, mas seu servo se regozijará.
29 Masu zargina za su sha kunya za a rufe su da kunya kamar mayafi.
Let meus adversários estão vestidos com desonra. Deixe-os se cobrir com sua própria vergonha como com um manto.
30 Da bakina zan ɗaukaka Ubangiji sosai; cikin babban taro zan yabe shi.
Vou agradecer muito a Iavé com minha boca. Sim, eu o elogiarei entre a multidão.
31 Gama yana tsaya a hannun damar mai bukata, don yă cece ransa daga waɗanda suke hukunta shi.
Pois ele estará à direita dos necessitados, para salvá-lo daqueles que julgam sua alma.

< Zabura 109 >