< Zabura 109 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda. Zabura ce. Ya Allah, wanda nake yabo, kada ka yi shiru,
Ó Deus do meu louvor, não te cales,
2 gama mugaye da masu ruɗu sun buɗe bakunansu a kaina; sun yi magana a kaina da harsunan ƙarya.
Pois a bocca do impio e a bocca do enganador estão abertas contra mim: teem fallado contra mim com uma lingua mentirosa.
3 Da kalmomin ƙiyayya sun kewaye ni; sun tasar mini ba dalili.
Elles me cercaram com palavras odiosas, e pelejaram contra mim sem causa.
4 A maimakon ƙauna sun sāka mini da zargi, amma ni mutum ne mai addu’a.
Em recompensa do meu amor são meus adversarios: mas eu faço oração.
5 Sun sāka mini alheri da mugunta, ƙauna kuma da ƙiyayya.
E me deram mal pelo bem, e odio pelo meu amor.
6 Ka naɗa mugun mutum yă yi hamayya da shi; bari mai zargi yă tsaya a hannun damansa.
Põe sobre elle um impio, e Satanaz esteja á sua direita.
7 Sa’ad da aka yi masa shari’a, bari a same shi da laifi, bari kuma addu’o’insa su hukunta shi.
Quando fôr julgado, saia condemnado; e a sua oração se lhe torne em peccado.
8 Bari kwanakinsa su zama kaɗan; bari wani yă ɗauki wurinsa na shugabanci.
Sejam poucos os seus dias, e outro tome o seu officio.
9 Bari’ya’yansa su zama marayu matarsa kuma gwauruwa.
Sejam orphãos os seus filhos, e viuva sua mulher.
10 Bari’ya’yansa su zama masu yawo suna bara; bari a yi ta koransu daga gidajensu da suke kufai.
Sejam vagabundos e pedintes os seus filhos, e busquem o pão dos seus logares desolados.
11 Bari mai binsa bashi yă ƙwace dukan abin da yake da shi; bari baƙi su washe amfanin aikinsa.
Lance o credor a mão a tudo quanto tenha, e despojem os estranhos o seu trabalho.
12 Bari kada kowa yă yi masa alheri ko yă ji tausayin marayunsa.
Não haja ninguem que se compadeça d'elle, nem haja quem favoreça os seus orphãos.
13 Bari duk zuriyarsa su mutu, a shafe sunayensu daga tsara mai zuwa.
Desappareça a sua posteridade, o seu nome seja apagado na seguinte geração.
14 Bari a tuna da laifin kakanninsa a gaban Ubangiji; bari kada a taɓa shafe zunubin mahaifiyarsa.
Esteja na memoria do Senhor a iniquidade de seus paes, e não se apague o peccado de sua mãe.
15 Bari zunubansu su kasance a gaban Ubangiji kullum, don yă sa a manta da su daga duniya.
Antes estejam sempre perante o Senhor, para que faça desapparecer a sua memoria da terra.
16 Gama bai taɓa yin tunanin yin alheri ba, amma ya tsananta wa matalauta da mabukata da kuma masu fid da zuciya har suka mutu.
Porquanto não se lembrou de fazer misericordia; antes perseguiu ao varão afflicto e ao necessitado, para que podesse até matar o quebrantado de coração.
17 Yana jin daɗin la’antarwa, bari yă dawo a kansa; ba ya son sa albarka, bari kada kowa yă sa masa albarka.
Visto que amou a maldição, ella lhe sobrevenha, e assim como não desejou a benção, ella se affaste d'elle.
18 Ya sa la’antarwa kamar rigarsa; ta shiga cikin jikinsa kamar ruwa, cikin ƙasusuwansa kamar mai.
Assim como se vestiu de maldição, como d'um vestido, assim penetre ella nas suas entranhas como agua, e em seus ossos como azeite.
19 Bari tă zama kamar mayafin da aka ɗaura kewaye da shi, kamar ɗamara da aka ɗaura kewaye da shi har abada.
Seja para elle como o vestido que o cobre, e como cinto que o cinja sempre.
20 Bari wannan yă zama sakayyar Ubangiji ga masu zargina, ga waɗanda suke mugayen maganganu a kaina.
Seja este o galardão dos meus contrarios, da parte do Senhor, e dos que fallam mal contra a minha alma.
21 Amma kai, ya Ubangiji Mai Iko Duka, ka yi da ni da kyau saboda sunanka; ta alherin ƙaunarka, ka cece ni.
Mas tu, Deus Senhor, trata comigo por amor do teu nome, porque a tua misericordia é boa; livra-me,
22 Gama ni matalauci ne mai bukata kuma, zuciyata kuwa ta yi rauni a cikina.
Pois estou afflicto e necessitado, e o meu coração está ferido dentro de mim.
23 Na ɓace kamar inuwar yamma; ana kakkaɓe ni kamar fāra.
Vou-me como a sombra que declina; sou sacudido como o gafanhoto.
24 Gwiwoyina suna mutuwa saboda azumi; jikina ya rame ba kuma ƙarfi.
De jejuar estão enfraquecidos os meus joelhos, e a minha carne emmagrece.
25 Na zama abin dariya ga masu zargina; sa’ad da suka gan ni, suka kaɗa kawunansu.
E ainda lhes sou opprobrio; quando me contemplam, movem as cabeças.
26 Ka taimake ni, ya Ubangiji Allahna; ka cece ni bisa ga ƙaunarka.
Ajuda-me, Senhor Deus meu, salva-me segundo a tua misericordia.
27 Bari su san cewa hannunka ne, cewa kai ne, ya Ubangiji, ka yi shi.
Para que saibam que esta é a tua mão, e que tu, Senhor, o fizeste.
28 Za su iya la’anta, amma kai za ka sa albarka; sa’ad da suka tasar za su sha kunya, amma bawanka zai yi farin ciki.
Amaldiçoem elles, mas abençoa tu: quando se levantarem fiquem confundidos; e alegre-se o teu servo.
29 Masu zargina za su sha kunya za a rufe su da kunya kamar mayafi.
Vistam-se os meus adversarios de vergonha, e cubram-se com a sua propria confusão como com uma capa.
30 Da bakina zan ɗaukaka Ubangiji sosai; cikin babban taro zan yabe shi.
Louvarei grandemente ao Senhor com a minha bocca: louval-o-hei entre a multidão.
31 Gama yana tsaya a hannun damar mai bukata, don yă cece ransa daga waɗanda suke hukunta shi.
Pois se porá á mão direita do pobre, para o livrar dos que condemnam a sua alma.

< Zabura 109 >