< Zabura 109 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda. Zabura ce. Ya Allah, wanda nake yabo, kada ka yi shiru,
in finem David psalmus
2 gama mugaye da masu ruɗu sun buɗe bakunansu a kaina; sun yi magana a kaina da harsunan ƙarya.
Deus laudem meam ne tacueris quia os peccatoris et os dolosi super me apertum est
3 Da kalmomin ƙiyayya sun kewaye ni; sun tasar mini ba dalili.
locuti sunt adversum me lingua dolosa et sermonibus odii circuierunt me et expugnaverunt me gratis
4 A maimakon ƙauna sun sāka mini da zargi, amma ni mutum ne mai addu’a.
pro eo ut me diligerent detrahebant mihi ego autem orabam
5 Sun sāka mini alheri da mugunta, ƙauna kuma da ƙiyayya.
et posuerunt adversus me mala pro bonis et odium pro dilectione mea
6 Ka naɗa mugun mutum yă yi hamayya da shi; bari mai zargi yă tsaya a hannun damansa.
constitue super eum peccatorem et diabulus stet a dextris eius
7 Sa’ad da aka yi masa shari’a, bari a same shi da laifi, bari kuma addu’o’insa su hukunta shi.
cum iudicatur exeat condemnatus et oratio eius fiat in peccatum
8 Bari kwanakinsa su zama kaɗan; bari wani yă ɗauki wurinsa na shugabanci.
fiant dies eius pauci et episcopatum eius accipiat alter
9 Bari’ya’yansa su zama marayu matarsa kuma gwauruwa.
fiant filii eius orfani et uxor eius vidua
10 Bari’ya’yansa su zama masu yawo suna bara; bari a yi ta koransu daga gidajensu da suke kufai.
nutantes transferantur filii eius et mendicent eiciantur de habitationibus suis
11 Bari mai binsa bashi yă ƙwace dukan abin da yake da shi; bari baƙi su washe amfanin aikinsa.
scrutetur fenerator omnem substantiam eius et diripiant alieni labores eius
12 Bari kada kowa yă yi masa alheri ko yă ji tausayin marayunsa.
non sit illi adiutor nec sit qui misereatur pupillis eius
13 Bari duk zuriyarsa su mutu, a shafe sunayensu daga tsara mai zuwa.
fiant nati eius in interitum in generatione una deleatur nomen eius
14 Bari a tuna da laifin kakanninsa a gaban Ubangiji; bari kada a taɓa shafe zunubin mahaifiyarsa.
in memoriam redeat iniquitas patrum eius in conspectu Domini et peccatum matris eius non deleatur
15 Bari zunubansu su kasance a gaban Ubangiji kullum, don yă sa a manta da su daga duniya.
fiant contra Dominum semper et dispereat de terra memoria eorum
16 Gama bai taɓa yin tunanin yin alheri ba, amma ya tsananta wa matalauta da mabukata da kuma masu fid da zuciya har suka mutu.
pro eo quod non est recordatus facere misericordiam
17 Yana jin daɗin la’antarwa, bari yă dawo a kansa; ba ya son sa albarka, bari kada kowa yă sa masa albarka.
et persecutus est hominem inopem et mendicum et conpunctum corde mortificare
18 Ya sa la’antarwa kamar rigarsa; ta shiga cikin jikinsa kamar ruwa, cikin ƙasusuwansa kamar mai.
et dilexit maledictionem et veniet ei et noluit benedictionem et elongabitur ab eo et induit maledictionem sicut vestimentum et intravit sicut aqua in interiora eius et sicut oleum in ossibus eius
19 Bari tă zama kamar mayafin da aka ɗaura kewaye da shi, kamar ɗamara da aka ɗaura kewaye da shi har abada.
fiat ei sicut vestimentum quo operitur et sicut zona qua semper praecingitur
20 Bari wannan yă zama sakayyar Ubangiji ga masu zargina, ga waɗanda suke mugayen maganganu a kaina.
hoc opus eorum qui detrahunt mihi apud Dominum et qui loquuntur mala adversus animam meam
21 Amma kai, ya Ubangiji Mai Iko Duka, ka yi da ni da kyau saboda sunanka; ta alherin ƙaunarka, ka cece ni.
et tu Domine Domine fac mecum propter nomen tuum quia suavis misericordia tua libera me
22 Gama ni matalauci ne mai bukata kuma, zuciyata kuwa ta yi rauni a cikina.
quia egenus et pauper ego sum et cor meum turbatum est intra me
23 Na ɓace kamar inuwar yamma; ana kakkaɓe ni kamar fāra.
sicut umbra cum declinat ablatus sum excussus sum sicut lucustae
24 Gwiwoyina suna mutuwa saboda azumi; jikina ya rame ba kuma ƙarfi.
genua mea infirmata sunt a ieiunio et caro mea inmutata est propter oleum
25 Na zama abin dariya ga masu zargina; sa’ad da suka gan ni, suka kaɗa kawunansu.
et ego factus sum obprobrium illis viderunt me moverunt capita sua
26 Ka taimake ni, ya Ubangiji Allahna; ka cece ni bisa ga ƙaunarka.
adiuva me Domine Deus meus salvum fac me secundum misericordiam tuam
27 Bari su san cewa hannunka ne, cewa kai ne, ya Ubangiji, ka yi shi.
et sciant quia manus tua haec tu Domine fecisti eam
28 Za su iya la’anta, amma kai za ka sa albarka; sa’ad da suka tasar za su sha kunya, amma bawanka zai yi farin ciki.
maledicent illi et tu benedices qui insurgunt in me confundantur servus autem tuus laetabitur
29 Masu zargina za su sha kunya za a rufe su da kunya kamar mayafi.
induantur qui detrahunt mihi pudore et operiantur sicut deploide confusione sua
30 Da bakina zan ɗaukaka Ubangiji sosai; cikin babban taro zan yabe shi.
confitebor Domino nimis in ore meo et in medio multorum laudabo eum
31 Gama yana tsaya a hannun damar mai bukata, don yă cece ransa daga waɗanda suke hukunta shi.
quia adstetit a dextris pauperis ut salvam faceret a persequentibus animam meam