< Zabura 109 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda. Zabura ce. Ya Allah, wanda nake yabo, kada ka yi shiru,
Dem Vorsänger. Ein Psalm Davids. Gott, den ich rühme, schweige nicht!
2 gama mugaye da masu ruɗu sun buɗe bakunansu a kaina; sun yi magana a kaina da harsunan ƙarya.
Denn sie haben ihr gottloses und falsches Maul wider mich aufgetan; sie sagen mir Lügen ins Gesicht,
3 Da kalmomin ƙiyayya sun kewaye ni; sun tasar mini ba dalili.
sie bieten gehässige Worte über mich herum und bekämpfen mich ohne Grund.
4 A maimakon ƙauna sun sāka mini da zargi, amma ni mutum ne mai addu’a.
Dafür, daß ich sie liebe, sind sie mir feind; ich aber bete.
5 Sun sāka mini alheri da mugunta, ƙauna kuma da ƙiyayya.
Sie beweisen mir Böses für Gutes und Haß für Liebe.
6 Ka naɗa mugun mutum yă yi hamayya da shi; bari mai zargi yă tsaya a hannun damansa.
Bestelle einen Gesetzlosen über ihn, und ein Ankläger stehe zu seiner Rechten!
7 Sa’ad da aka yi masa shari’a, bari a same shi da laifi, bari kuma addu’o’insa su hukunta shi.
Wenn er gerichtet wird, so möge er schuldig gesprochen werden, und sein Gebet werde ihm zur Sünde!
8 Bari kwanakinsa su zama kaɗan; bari wani yă ɗauki wurinsa na shugabanci.
Seiner Tage seien wenige, und sein Amt empfange ein anderer!
9 Bari’ya’yansa su zama marayu matarsa kuma gwauruwa.
Seine Kinder sollen Waisen werden und sein Weib eine Witwe!
10 Bari’ya’yansa su zama masu yawo suna bara; bari a yi ta koransu daga gidajensu da suke kufai.
Seine Kinder müssen umherwanken und betteln, hilfesuchend aus ihren Ruinen hervorkommen!
11 Bari mai binsa bashi yă ƙwace dukan abin da yake da shi; bari baƙi su washe amfanin aikinsa.
Der Gläubiger nehme ihm alles weg, und Fremde sollen plündern, was er sich erworben.
12 Bari kada kowa yă yi masa alheri ko yă ji tausayin marayunsa.
Niemand gebe ihm Gnadenfrist, und keiner erbarme sich seiner Waisen!
13 Bari duk zuriyarsa su mutu, a shafe sunayensu daga tsara mai zuwa.
Seine Nachkommenschaft falle der Ausrottung anheim, ihr Name erlösche im zweiten Geschlecht!
14 Bari a tuna da laifin kakanninsa a gaban Ubangiji; bari kada a taɓa shafe zunubin mahaifiyarsa.
Seiner Väter Missetat müsse gedacht werden vor dem HERRN, und seiner Mutter Sünde werde nicht ausgetilgt!
15 Bari zunubansu su kasance a gaban Ubangiji kullum, don yă sa a manta da su daga duniya.
Der HERR habe sie beständig vor Augen, daß ihr Gedächtnis von der Erde vertilgt werde,
16 Gama bai taɓa yin tunanin yin alheri ba, amma ya tsananta wa matalauta da mabukata da kuma masu fid da zuciya har suka mutu.
weil er nicht daran dachte, Barmherzigkeit zu üben, sondern den Elenden und Armen verfolgte und den Niedergeschlagenen, um ihn in den Tod zu treiben.
17 Yana jin daɗin la’antarwa, bari yă dawo a kansa; ba ya son sa albarka, bari kada kowa yă sa masa albarka.
Da er den Fluch liebte, so komme er über ihn; und da er den Segen nicht begehrte, so sei er fern von ihm!
18 Ya sa la’antarwa kamar rigarsa; ta shiga cikin jikinsa kamar ruwa, cikin ƙasusuwansa kamar mai.
Er zog den Fluch an wie sein Gewand; so dringe er in sein Inneres wie Wasser und wie Öl in seine Gebeine;
19 Bari tă zama kamar mayafin da aka ɗaura kewaye da shi, kamar ɗamara da aka ɗaura kewaye da shi har abada.
er sei ihm wie das Kleid, das er anzieht, und wie der Gurt, damit er sich ständig umgürtet!
20 Bari wannan yă zama sakayyar Ubangiji ga masu zargina, ga waɗanda suke mugayen maganganu a kaina.
Das sei der Lohn meiner Ankläger vonseiten des HERRN, derer, welche Arges wider meine Seele reden!
21 Amma kai, ya Ubangiji Mai Iko Duka, ka yi da ni da kyau saboda sunanka; ta alherin ƙaunarka, ka cece ni.
Du aber, o HERR, mein Herr, handle mit mir um deines Namens willen; denn deine Gnade ist gut; darum errette mich!
22 Gama ni matalauci ne mai bukata kuma, zuciyata kuwa ta yi rauni a cikina.
Denn ich bin elend und arm, und mein Herz ist verwundet in meiner Brust.
23 Na ɓace kamar inuwar yamma; ana kakkaɓe ni kamar fāra.
Wie ein Schatten, wenn er sich neigt, schleiche ich dahin; ich werde verscheucht wie eine Heuschrecke.
24 Gwiwoyina suna mutuwa saboda azumi; jikina ya rame ba kuma ƙarfi.
Meine Knie wanken vom Fasten, mein Fleisch magert gänzlich ab;
25 Na zama abin dariya ga masu zargina; sa’ad da suka gan ni, suka kaɗa kawunansu.
und ich bin ihnen zum Gespött geworden; wer mich sieht, schüttelt den Kopf.
26 Ka taimake ni, ya Ubangiji Allahna; ka cece ni bisa ga ƙaunarka.
Hilf mir, o HERR, mein Gott! Rette mich nach deiner Gnade,
27 Bari su san cewa hannunka ne, cewa kai ne, ya Ubangiji, ka yi shi.
so wird man erkennen, daß dies deine Hand ist, daß du, HERR, solches getan hast.
28 Za su iya la’anta, amma kai za ka sa albarka; sa’ad da suka tasar za su sha kunya, amma bawanka zai yi farin ciki.
Fluchen sie, so segne du; setzen sie sich wider mich, so müssen sie zuschanden werden; aber dein Knecht müsse sich freuen.
29 Masu zargina za su sha kunya za a rufe su da kunya kamar mayafi.
Meine Ankläger müssen Schmach anziehen und in ihre Schande sich hüllen wie in einen Mantel.
30 Da bakina zan ɗaukaka Ubangiji sosai; cikin babban taro zan yabe shi.
Ich will den HERRN laut preisen mit meinem Munde und inmitten vieler ihn rühmen,
31 Gama yana tsaya a hannun damar mai bukata, don yă cece ransa daga waɗanda suke hukunta shi.
weil er dem Armen zur Seite steht, ihn zu retten von denen, die ihn verurteilen.