< Zabura 109 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda. Zabura ce. Ya Allah, wanda nake yabo, kada ka yi shiru,
Psaume de David, [donné] au maître chantre. Ô Dieu de ma louange, ne te tais point.
2 gama mugaye da masu ruɗu sun buɗe bakunansu a kaina; sun yi magana a kaina da harsunan ƙarya.
Car la bouche du méchant, et la bouche [remplie] de fraudes se sont ouvertes contre moi, [et] m'ont parlé, en usant d'une langue trompeuse.
3 Da kalmomin ƙiyayya sun kewaye ni; sun tasar mini ba dalili.
Et des paroles pleines de haine m'ont environné, et ils me font la guerre sans cause.
4 A maimakon ƙauna sun sāka mini da zargi, amma ni mutum ne mai addu’a.
Au lieu que je les aimais, ils ont été mes ennemis; mais moi, je n'ai fait que prier [en leur faveur].
5 Sun sāka mini alheri da mugunta, ƙauna kuma da ƙiyayya.
Et ils m'ont rendu le mal pour le bien, et la haine pour l'amour que je leur portais.
6 Ka naɗa mugun mutum yă yi hamayya da shi; bari mai zargi yă tsaya a hannun damansa.
Etablis le méchant sur lui, et fais que l'adversaire se tienne à sa droite.
7 Sa’ad da aka yi masa shari’a, bari a same shi da laifi, bari kuma addu’o’insa su hukunta shi.
Quand il sera jugé, fais qu'il soit déclaré méchant, et que sa prière soit regardée comme un crime.
8 Bari kwanakinsa su zama kaɗan; bari wani yă ɗauki wurinsa na shugabanci.
Que sa vie soit courte, et qu'un autre prenne sa charge.
9 Bari’ya’yansa su zama marayu matarsa kuma gwauruwa.
Que ses enfants soient orphelins, et sa femme veuve;
10 Bari’ya’yansa su zama masu yawo suna bara; bari a yi ta koransu daga gidajensu da suke kufai.
Et que ses enfants soient entièrement vagabonds, et qu'ils mendient et quêtent [en sortant] de leurs maisons détruites.
11 Bari mai binsa bashi yă ƙwace dukan abin da yake da shi; bari baƙi su washe amfanin aikinsa.
Que le créancier usant d'exaction attrape tout ce qui est à lui, et que les étrangers butinent tout son travail.
12 Bari kada kowa yă yi masa alheri ko yă ji tausayin marayunsa.
Qu'il n'y ait personne qui étende sa compassion sur lui, et qu'il n'y ait personne qui ait pitié de ses orphelins.
13 Bari duk zuriyarsa su mutu, a shafe sunayensu daga tsara mai zuwa.
Que sa postérité soit exposée à être retranchée; que leur nom soit effacé dans la race qui le suivra.
14 Bari a tuna da laifin kakanninsa a gaban Ubangiji; bari kada a taɓa shafe zunubin mahaifiyarsa.
Que l'iniquité de ses pères revienne en mémoire à l'Eternel, et que le péché de sa mère ne soit point effacé.
15 Bari zunubansu su kasance a gaban Ubangiji kullum, don yă sa a manta da su daga duniya.
Qu'ils soient continuellement devant l'Eternel; et qu'il retranche leur mémoire de la terre;
16 Gama bai taɓa yin tunanin yin alheri ba, amma ya tsananta wa matalauta da mabukata da kuma masu fid da zuciya har suka mutu.
Parce qu'il ne s'est point souvenu d'user de miséricorde, mais il a persécuté l'homme affligé et misérable, dont le cœur est brisé, et cela pour le faire mourir.
17 Yana jin daɗin la’antarwa, bari yă dawo a kansa; ba ya son sa albarka, bari kada kowa yă sa masa albarka.
Puisqu'il a aimé la malédiction, que la malédiction tombe sur lui; et parce qu'il n'a point pris plaisir à la bénédiction, que la bénédiction aussi s'éloigne de lui.
18 Ya sa la’antarwa kamar rigarsa; ta shiga cikin jikinsa kamar ruwa, cikin ƙasusuwansa kamar mai.
Et qu'il soit revêtu de malédiction comme de sa robe, et qu'elle entre dans son corps comme de l'eau, et dans ses os comme de l'huile.
19 Bari tă zama kamar mayafin da aka ɗaura kewaye da shi, kamar ɗamara da aka ɗaura kewaye da shi har abada.
Qu'elle lui soit comme un vêtement dont il se couvre, et comme une ceinture, dont il se ceigne continuellement.
20 Bari wannan yă zama sakayyar Ubangiji ga masu zargina, ga waɗanda suke mugayen maganganu a kaina.
Telle soit de part l'Eternel la récompense de mes adversaires, et de ceux qui parlent mal de moi.
21 Amma kai, ya Ubangiji Mai Iko Duka, ka yi da ni da kyau saboda sunanka; ta alherin ƙaunarka, ka cece ni.
Mais toi, Eternel Seigneur, agis avec moi pour l'amour de ton Nom; [et] parce que ta miséricorde est tendre, délivre-moi.
22 Gama ni matalauci ne mai bukata kuma, zuciyata kuwa ta yi rauni a cikina.
Car je suis affligé et misérable, et mon cœur est blessé au-dedans de moi.
23 Na ɓace kamar inuwar yamma; ana kakkaɓe ni kamar fāra.
Je m'en vais comme l'ombre quand elle décline, et je suis chassé comme une sauterelle.
24 Gwiwoyina suna mutuwa saboda azumi; jikina ya rame ba kuma ƙarfi.
Mes genoux sont affaiblis par le jeûne, et ma chair s'est amaigrie, au lieu qu'elle était en bon point.
25 Na zama abin dariya ga masu zargina; sa’ad da suka gan ni, suka kaɗa kawunansu.
Encore leur suis-je en opprobre; quand ils me voient ils branlent la tête.
26 Ka taimake ni, ya Ubangiji Allahna; ka cece ni bisa ga ƙaunarka.
Eternel mon Dieu! aide-moi, [et] délivre-moi selon ta miséricorde.
27 Bari su san cewa hannunka ne, cewa kai ne, ya Ubangiji, ka yi shi.
Afin qu'on connaisse que c'est ici ta main, et que toi, ô Eternel! tu as fait ceci.
28 Za su iya la’anta, amma kai za ka sa albarka; sa’ad da suka tasar za su sha kunya, amma bawanka zai yi farin ciki.
Ils maudiront, mais tu béniras; ils s'élèveront, mais ils seront confus, et ton serviteur se réjouira.
29 Masu zargina za su sha kunya za a rufe su da kunya kamar mayafi.
Que mes adversaires soient revêtus de confusion, et couverts de leur honte comme d'un manteau.
30 Da bakina zan ɗaukaka Ubangiji sosai; cikin babban taro zan yabe shi.
Je célébrerai hautement de ma bouche l'Eternel, et je le louerai au milieu de plusieurs nations.
31 Gama yana tsaya a hannun damar mai bukata, don yă cece ransa daga waɗanda suke hukunta shi.
De ce qu'il se tient à la droite du misérable, pour le délivrer de ceux qui condamnent son âme.

< Zabura 109 >