< Zabura 109 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda. Zabura ce. Ya Allah, wanda nake yabo, kada ka yi shiru,
Au chef des chantres. De David. Psaume. Dieu, objet de mes louanges, ne garde pas le silence!
2 gama mugaye da masu ruɗu sun buɗe bakunansu a kaina; sun yi magana a kaina da harsunan ƙarya.
Car la bouche du méchant, la bouche de la fourberie s’ouvrent contre moi; on me parle un langage mensonger.
3 Da kalmomin ƙiyayya sun kewaye ni; sun tasar mini ba dalili.
On m’enveloppe de propos haineux, on me fait la guerre sans motif.
4 A maimakon ƙauna sun sāka mini da zargi, amma ni mutum ne mai addu’a.
En échange de mon amour, on me traite en ennemi, et moi je ne suis que prière.
5 Sun sāka mini alheri da mugunta, ƙauna kuma da ƙiyayya.
On me rend le mal pour le bien, la haine est le prix de mon affection.
6 Ka naɗa mugun mutum yă yi hamayya da shi; bari mai zargi yă tsaya a hannun damansa.
Suscite un méchant contre lui, qu’un accusateur se dresse à sa droite!
7 Sa’ad da aka yi masa shari’a, bari a same shi da laifi, bari kuma addu’o’insa su hukunta shi.
Quand il passe en jugement, qu’il s’en revienne condamné! Que sa prière lui soit imputée à péché!
8 Bari kwanakinsa su zama kaɗan; bari wani yă ɗauki wurinsa na shugabanci.
Que ses jours soient peu nombreux, qu’un autre s’empare de son office!
9 Bari’ya’yansa su zama marayu matarsa kuma gwauruwa.
Que ses enfants soient orphelins, que sa femme devienne veuve.
10 Bari’ya’yansa su zama masu yawo suna bara; bari a yi ta koransu daga gidajensu da suke kufai.
Que ses enfants errent de tous côtés pour mendier, qu’ils sollicitent, éloignés des ruines de leur demeure.
11 Bari mai binsa bashi yă ƙwace dukan abin da yake da shi; bari baƙi su washe amfanin aikinsa.
Que le créancier saisisse tout son avoir, que des étrangers mettent au pillage le fruit de son labeur.
12 Bari kada kowa yă yi masa alheri ko yă ji tausayin marayunsa.
Qu’il n’y ait personne pour lui tendre une main secourable, personne pour avoir compassion de ses orphelins.
13 Bari duk zuriyarsa su mutu, a shafe sunayensu daga tsara mai zuwa.
Que sa postérité soit condamnée à disparaître, qu’à la génération prochaine son nom soit éteint.
14 Bari a tuna da laifin kakanninsa a gaban Ubangiji; bari kada a taɓa shafe zunubin mahaifiyarsa.
Que l’iniquité de ses pères soit présente au souvenir de l’Eternel. Que jamais ne s’efface la faute de sa mère.
15 Bari zunubansu su kasance a gaban Ubangiji kullum, don yă sa a manta da su daga duniya.
Que le Seigneur les ait toujours sous les yeux, et extirpe leur mémoire de la terre;
16 Gama bai taɓa yin tunanin yin alheri ba, amma ya tsananta wa matalauta da mabukata da kuma masu fid da zuciya har suka mutu.
parce qu’il n’a pas songé à pratiquer la charité, qu’il a persécuté un homme malheureux, déshérité, au cœur brisé pour amener sa perte.
17 Yana jin daɗin la’antarwa, bari yă dawo a kansa; ba ya son sa albarka, bari kada kowa yă sa masa albarka.
Il a aimé la malédiction: elle est venue le frapper; il n’avait aucun goût pour la bénédiction: elle l’a fui.
18 Ya sa la’antarwa kamar rigarsa; ta shiga cikin jikinsa kamar ruwa, cikin ƙasusuwansa kamar mai.
Il a endossé la malédiction comme sa tunique; elle a pénétré en son sein comme de l’eau, comme de l’huile dans ses membres.
19 Bari tă zama kamar mayafin da aka ɗaura kewaye da shi, kamar ɗamara da aka ɗaura kewaye da shi har abada.
Qu’elle soit donc pour lui comme un vêtement dont il s’enveloppe, qu’elle l’entoure comme d’une perpétuelle ceinture.
20 Bari wannan yă zama sakayyar Ubangiji ga masu zargina, ga waɗanda suke mugayen maganganu a kaina.
Que tel soit, de par l’Eternel, le salaire de mes adversaires, de ceux qui débitent des méchancetés contre moi!
21 Amma kai, ya Ubangiji Mai Iko Duka, ka yi da ni da kyau saboda sunanka; ta alherin ƙaunarka, ka cece ni.
Mais toi, Eternel, Seigneur, traite-moi comme l’exige l’honneur de ton nom, car précieuse est ta grâce: sauve-moi!
22 Gama ni matalauci ne mai bukata kuma, zuciyata kuwa ta yi rauni a cikina.
Je suis, en effet, pauvre et misérable, et mon cœur est déchiré en moi.
23 Na ɓace kamar inuwar yamma; ana kakkaɓe ni kamar fāra.
Pareil à l’ombre qui s’allonge, je m’évanouis, je suis pourchassé comme par une nuée de sauterelles.
24 Gwiwoyina suna mutuwa saboda azumi; jikina ya rame ba kuma ƙarfi.
Mes genoux flageolent, épuisés par le jeûne; mon corps est amaigri, a perdu toute graisse.
25 Na zama abin dariya ga masu zargina; sa’ad da suka gan ni, suka kaɗa kawunansu.
Et je suis devenu pour eux un objet d’opprobre, ils me regardent et hochent la tête.
26 Ka taimake ni, ya Ubangiji Allahna; ka cece ni bisa ga ƙaunarka.
Secours-moi, Eternel, mon Dieu, accorde-moi ton aide en raison de ta bonté.
27 Bari su san cewa hannunka ne, cewa kai ne, ya Ubangiji, ka yi shi.
Qu’on sache que cela vient de ta main, que toi, ô Seigneur, tu as tout fait.
28 Za su iya la’anta, amma kai za ka sa albarka; sa’ad da suka tasar za su sha kunya, amma bawanka zai yi farin ciki.
Qu’ils maudissent, eux, toi, tu béniras; qu’ils se lèvent, ils seront couverts de honte, et ton serviteur sera dans la joie.
29 Masu zargina za su sha kunya za a rufe su da kunya kamar mayafi.
Que mes adversaires se revêtent d’ignominie, qu’ils soient enveloppés de leur honte comme d’un manteau.
30 Da bakina zan ɗaukaka Ubangiji sosai; cikin babban taro zan yabe shi.
Ma bouche abondera en actions de grâce à l’Eternel; au milieu des foules, je proclamerai ses louanges.
31 Gama yana tsaya a hannun damar mai bukata, don yă cece ransa daga waɗanda suke hukunta shi.
Car il se tient à la droite du malheureux, pour l’assister contre ceux qui condamnent sa personne.