< Zabura 109 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda. Zabura ce. Ya Allah, wanda nake yabo, kada ka yi shiru,
God, you are the one whom I praise, [So please] answer [my prayer],
2 gama mugaye da masu ruɗu sun buɗe bakunansu a kaina; sun yi magana a kaina da harsunan ƙarya.
because wicked people slander me and tell [MTY] lies about me.
3 Da kalmomin ƙiyayya sun kewaye ni; sun tasar mini ba dalili.
They are constantly saying that they hate me, and they say evil things about me for no reason.
4 A maimakon ƙauna sun sāka mini da zargi, amma ni mutum ne mai addu’a.
I show them that I want to be their friends and I pray for them, but [instead of being kind to me], they say that I have done evil things.
5 Sun sāka mini alheri da mugunta, ƙauna kuma da ƙiyayya.
In return for my doing good things for them and loving them, they do evil things to me and hate me.
6 Ka naɗa mugun mutum yă yi hamayya da shi; bari mai zargi yă tsaya a hannun damansa.
They said, “Appoint a wicked [judge] who will judge him, and bring in one of his enemies who will stand up and accuse him.
7 Sa’ad da aka yi masa shari’a, bari a same shi da laifi, bari kuma addu’o’insa su hukunta shi.
And cause that when the trial [ends], [the judge will] declare that he is guilty, and that [even] his prayer will be considered to be a sin.
8 Bari kwanakinsa su zama kaɗan; bari wani yă ɗauki wurinsa na shugabanci.
[Then], cause that he will soon die and that someone else will have his job/work (OR, possessions).
9 Bari’ya’yansa su zama marayu matarsa kuma gwauruwa.
Cause that his children will not have a father any more and that his wife will become a widow.
10 Bari’ya’yansa su zama masu yawo suna bara; bari a yi ta koransu daga gidajensu da suke kufai.
Cause that his children will be forced to leave the ruined homes that they have been living in and wander around begging for food.
11 Bari mai binsa bashi yă ƙwace dukan abin da yake da shi; bari baƙi su washe amfanin aikinsa.
Cause that all the people to whom he owed money will seize all his property; Cause that strangers will take away everything that he worked to acquire.
12 Bari kada kowa yă yi masa alheri ko yă ji tausayin marayunsa.
Cause that [while he is still living] no one will be kind to him, and [after he dies], cause that no one will pity his children.
13 Bari duk zuriyarsa su mutu, a shafe sunayensu daga tsara mai zuwa.
Cause that all his descendants will die and that his grandchildren will not remember who he [MTY] was.
14 Bari a tuna da laifin kakanninsa a gaban Ubangiji; bari kada a taɓa shafe zunubin mahaifiyarsa.
Yahweh, remember [and do not forgive] his ancestors for the evil things that they did, and do not [even] forgive the sins that his mother committed;
15 Bari zunubansu su kasance a gaban Ubangiji kullum, don yă sa a manta da su daga duniya.
think about his sins continually, and cause that his name will be completely forgotten.
16 Gama bai taɓa yin tunanin yin alheri ba, amma ya tsananta wa matalauta da mabukata da kuma masu fid da zuciya har suka mutu.
He never was kind to anyone; he (persecuted/cause problems for) poor and needy [people] and even killed helpless [people].
17 Yana jin daɗin la’antarwa, bari yă dawo a kansa; ba ya son sa albarka, bari kada kowa yă sa masa albarka.
He liked to curse [people]. [So] cause those terrible things that he requested to happen to others to happen to him! He did not want to bless [others], [so] cause that no one will bless him!
18 Ya sa la’antarwa kamar rigarsa; ta shiga cikin jikinsa kamar ruwa, cikin ƙasusuwansa kamar mai.
He cursed other people [as often/easily] as he put on his clothes [SIM]; cause that the terrible things that he wanted to happen to others will [happen to him and] enter his body like water [that he drinks] [SIM], like [olive] oil soaks into a person’s bones [when it is rubbed on his skin] [SIM].
19 Bari tă zama kamar mayafin da aka ɗaura kewaye da shi, kamar ɗamara da aka ɗaura kewaye da shi har abada.
Cause that those terrible things will cling to him like his clothes and be around him like the belt that he wears every day.”
20 Bari wannan yă zama sakayyar Ubangiji ga masu zargina, ga waɗanda suke mugayen maganganu a kaina.
Yahweh, I want you to punish all my enemies that way, those who say evil things about me.
21 Amma kai, ya Ubangiji Mai Iko Duka, ka yi da ni da kyau saboda sunanka; ta alherin ƙaunarka, ka cece ni.
But Yahweh, my God, do good things for me in order that I may honor you; rescue me [from my enemies] because your faithfully loving me is good.
22 Gama ni matalauci ne mai bukata kuma, zuciyata kuwa ta yi rauni a cikina.
[I ask you to do this] because I am poor and needy and my inner being is (full of pain/very troubled/discouraged).
23 Na ɓace kamar inuwar yamma; ana kakkaɓe ni kamar fāra.
[I think that] my time [to remain alive] is short, like an evening shadow [that will soon disappear] [SIM]. I will be blown away like a locust/grasshopper is blown [by the wind].
24 Gwiwoyina suna mutuwa saboda azumi; jikina ya rame ba kuma ƙarfi.
My knees are weak because I have (fasted/abstained from eating food) very often, and my body has become very thin.
25 Na zama abin dariya ga masu zargina; sa’ad da suka gan ni, suka kaɗa kawunansu.
The people who accuse me make fun of me; when they see me, they [insult me by] shaking their heads [at me as though I were an evil man].
26 Ka taimake ni, ya Ubangiji Allahna; ka cece ni bisa ga ƙaunarka.
Yahweh, my God, help me! Because you faithfully love [me], rescue me!
27 Bari su san cewa hannunka ne, cewa kai ne, ya Ubangiji, ka yi shi.
[When you save me], cause my enemies to know that you are the one who has done it!
28 Za su iya la’anta, amma kai za ka sa albarka; sa’ad da suka tasar za su sha kunya, amma bawanka zai yi farin ciki.
They may curse me, but I ask that you bless me. Cause those who (persecute/cause problems for) me [to be defeated and as a result] to be disgraced/ashamed, and cause me to be glad/happy!
29 Masu zargina za su sha kunya za a rufe su da kunya kamar mayafi.
Cause those who accuse me to be completely disgraced; cause [other people to see] that they are disgraced, as [easily as they see] the clothes that they wear [SIM]!
30 Da bakina zan ɗaukaka Ubangiji sosai; cikin babban taro zan yabe shi.
But I will thank Yahweh very greatly; I will praise him [when I am] among the crowd [of people who are worshiping him].
31 Gama yana tsaya a hannun damar mai bukata, don yă cece ransa daga waɗanda suke hukunta shi.
[I will do that] because he defends [MTY] needy [people like me], and saves us from those who have decided/declared that we must be executed.

< Zabura 109 >