< Zabura 109 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda. Zabura ce. Ya Allah, wanda nake yabo, kada ka yi shiru,
To the choirmaster of David a psalm O God of praise my may not you be silent.
2 gama mugaye da masu ruɗu sun buɗe bakunansu a kaina; sun yi magana a kaina da harsunan ƙarya.
For [the] mouth of [the] wicked and a mouth of deceit on me they have opened they have spoken with me a tongue of falsehood.
3 Da kalmomin ƙiyayya sun kewaye ni; sun tasar mini ba dalili.
And words of hatred they have surrounded me and they have fought against me without cause.
4 A maimakon ƙauna sun sāka mini da zargi, amma ni mutum ne mai addu’a.
In place of love my they accuse me and I [am] prayer.
5 Sun sāka mini alheri da mugunta, ƙauna kuma da ƙiyayya.
And they have put on me evil in place of good and hatred in place of love my.
6 Ka naɗa mugun mutum yă yi hamayya da shi; bari mai zargi yă tsaya a hannun damansa.
Appoint on him a wicked [person] and an accuser let him stand on right [hand] his.
7 Sa’ad da aka yi masa shari’a, bari a same shi da laifi, bari kuma addu’o’insa su hukunta shi.
When is judged he let him come forth guilty and prayer his let it become sin.
8 Bari kwanakinsa su zama kaɗan; bari wani yă ɗauki wurinsa na shugabanci.
May they be days his few office his may he take another.
9 Bari’ya’yansa su zama marayu matarsa kuma gwauruwa.
May they be children his fatherless ones and wife his a widow.
10 Bari’ya’yansa su zama masu yawo suna bara; bari a yi ta koransu daga gidajensu da suke kufai.
And really may they wander children his and they will beg and they will seek away from ruins their.
11 Bari mai binsa bashi yă ƙwace dukan abin da yake da shi; bari baƙi su washe amfanin aikinsa.
May he strike a creditor to all that [belongs] to him and may they plunder strangers property his.
12 Bari kada kowa yă yi masa alheri ko yă ji tausayin marayunsa.
May not it belong to him [one who] prolongs loyalty and may not it belong [one who] shows favor to fatherless children his.
13 Bari duk zuriyarsa su mutu, a shafe sunayensu daga tsara mai zuwa.
May it be posterity his to cut off in a generation another may it be wiped out name their.
14 Bari a tuna da laifin kakanninsa a gaban Ubangiji; bari kada a taɓa shafe zunubin mahaifiyarsa.
May it be remembered - [the] iniquity of ancestors his to Yahweh and [the] sin of mother his may not it be wiped out.
15 Bari zunubansu su kasance a gaban Ubangiji kullum, don yă sa a manta da su daga duniya.
Let them be before Yahweh continually and may he cut off from [the] earth memory their.
16 Gama bai taɓa yin tunanin yin alheri ba, amma ya tsananta wa matalauta da mabukata da kuma masu fid da zuciya har suka mutu.
Because that - not he remembered to do loyalty and he harassed anyone poor and needy and disheartened of heart to put to [them] death.
17 Yana jin daɗin la’antarwa, bari yă dawo a kansa; ba ya son sa albarka, bari kada kowa yă sa masa albarka.
And he loved a curse and it came to him and not he delighted in blessing and it was far from him.
18 Ya sa la’antarwa kamar rigarsa; ta shiga cikin jikinsa kamar ruwa, cikin ƙasusuwansa kamar mai.
And he put on a curse like garment his and it went like water in inward part[s] his and like oil in bones his.
19 Bari tă zama kamar mayafin da aka ɗaura kewaye da shi, kamar ɗamara da aka ɗaura kewaye da shi har abada.
May it be for him like a garment [which] he wraps himself and to a waistband [which] continually he girds on it.
20 Bari wannan yă zama sakayyar Ubangiji ga masu zargina, ga waɗanda suke mugayen maganganu a kaina.
This [be] [the] wage[s] of accusers my from with Yahweh and those [who] speak evil on self my.
21 Amma kai, ya Ubangiji Mai Iko Duka, ka yi da ni da kyau saboda sunanka; ta alherin ƙaunarka, ka cece ni.
And you - O Yahweh O Lord deal with me for [the] sake of name your for [is] good covenant loyalty your deliver me.
22 Gama ni matalauci ne mai bukata kuma, zuciyata kuwa ta yi rauni a cikina.
For [am] poor and needy I and heart my someone has pierced in inner being my.
23 Na ɓace kamar inuwar yamma; ana kakkaɓe ni kamar fāra.
Like a shadow when stretches out it I have vanished I have been shaken off like locust.
24 Gwiwoyina suna mutuwa saboda azumi; jikina ya rame ba kuma ƙarfi.
Knees my they have staggered from fasting and flesh my it has become lean from fatness.
25 Na zama abin dariya ga masu zargina; sa’ad da suka gan ni, suka kaɗa kawunansu.
And I - I have become a reproach to them they see me they shake! head their.
26 Ka taimake ni, ya Ubangiji Allahna; ka cece ni bisa ga ƙaunarka.
Help me O Yahweh God my save me according to covenant loyalty your.
27 Bari su san cewa hannunka ne, cewa kai ne, ya Ubangiji, ka yi shi.
So they may know that [is] hand your this you O Yahweh you have done it.
28 Za su iya la’anta, amma kai za ka sa albarka; sa’ad da suka tasar za su sha kunya, amma bawanka zai yi farin ciki.
They will curse they and you you will bless they have arisen - and they have been ashamed and servant your he will rejoice.
29 Masu zargina za su sha kunya za a rufe su da kunya kamar mayafi.
May they be clothed accusers my ignominy and may they be wrapped like robe shame their.
30 Da bakina zan ɗaukaka Ubangiji sosai; cikin babban taro zan yabe shi.
I will give thanks to Yahweh exceedingly with mouth my and in among many [people] I will praise him.
31 Gama yana tsaya a hannun damar mai bukata, don yă cece ransa daga waɗanda suke hukunta shi.
For he stands to [the] right [hand] of [the] needy to save [him] from [those who] judge self his.

< Zabura 109 >