< Zabura 109 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda. Zabura ce. Ya Allah, wanda nake yabo, kada ka yi shiru,
“To the chief musician, by David, a psalm.” O God of my praise, do not keep silence.
2 gama mugaye da masu ruɗu sun buɗe bakunansu a kaina; sun yi magana a kaina da harsunan ƙarya.
For the mouth of the wicked and the mouth of deceit are opened against me: they have spoken with me with the tongue of falsehood.
3 Da kalmomin ƙiyayya sun kewaye ni; sun tasar mini ba dalili.
Also with words of hatred have they encompassed me, and they fight against me without a cause.
4 A maimakon ƙauna sun sāka mini da zargi, amma ni mutum ne mai addu’a.
In recompense for my love are they my accusers, while I have nothing but prayer.
5 Sun sāka mini alheri da mugunta, ƙauna kuma da ƙiyayya.
And they impose evil on me in recompense for good, and hatred in lieu of my love.
6 Ka naɗa mugun mutum yă yi hamayya da shi; bari mai zargi yă tsaya a hannun damansa.
Appoint thou a wicked man over him: and let an accuser stand at his right hand.
7 Sa’ad da aka yi masa shari’a, bari a same shi da laifi, bari kuma addu’o’insa su hukunta shi.
When he is to be judged, let him go forth guilty, and let his prayer become sin.
8 Bari kwanakinsa su zama kaɗan; bari wani yă ɗauki wurinsa na shugabanci.
Let his days be few, and let another take his office.
9 Bari’ya’yansa su zama marayu matarsa kuma gwauruwa.
Let his children be fatherless, and his wife a widow.
10 Bari’ya’yansa su zama masu yawo suna bara; bari a yi ta koransu daga gidajensu da suke kufai.
Let his children be continually moving about, and beg, and let them seek [their bread] out of their ruined places.
11 Bari mai binsa bashi yă ƙwace dukan abin da yake da shi; bari baƙi su washe amfanin aikinsa.
Let the creditor lay snares after all that he hath, and let strangers plunder his labor.
12 Bari kada kowa yă yi masa alheri ko yă ji tausayin marayunsa.
Let him have none that extendeth kindness, and let there be none that is gracious to his fatherless children.
13 Bari duk zuriyarsa su mutu, a shafe sunayensu daga tsara mai zuwa.
Let his posterity be cut off: in another generation let their name be blotted out.
14 Bari a tuna da laifin kakanninsa a gaban Ubangiji; bari kada a taɓa shafe zunubin mahaifiyarsa.
Let the iniquity of his fathers be remembered by the Lord, and let the sin of his mother not be blotted out.
15 Bari zunubansu su kasance a gaban Ubangiji kullum, don yă sa a manta da su daga duniya.
Let them be before the Lord continually, that he may cut off from the earth their memory.
16 Gama bai taɓa yin tunanin yin alheri ba, amma ya tsananta wa matalauta da mabukata da kuma masu fid da zuciya har suka mutu.
For the reason that he remembered not to show kindness; but persecuted the poor and needy man, and the grieved in heart to put him to death.
17 Yana jin daɗin la’antarwa, bari yă dawo a kansa; ba ya son sa albarka, bari kada kowa yă sa masa albarka.
As he loved cursing, so let it come over him: and as he delighted not in blessing, so let it be far from him.
18 Ya sa la’antarwa kamar rigarsa; ta shiga cikin jikinsa kamar ruwa, cikin ƙasusuwansa kamar mai.
And he clothed himself with cursing as with his garment, and it cometh like water within him, and like oil into his bones.
19 Bari tă zama kamar mayafin da aka ɗaura kewaye da shi, kamar ɗamara da aka ɗaura kewaye da shi har abada.
Let it be unto him as a garment in which he wrappeth himself, and for a girdle let him be continually girded with it.
20 Bari wannan yă zama sakayyar Ubangiji ga masu zargina, ga waɗanda suke mugayen maganganu a kaina.
Let this be the reward of my accusers from the Lord, and of those that speak evil against my soul.
21 Amma kai, ya Ubangiji Mai Iko Duka, ka yi da ni da kyau saboda sunanka; ta alherin ƙaunarka, ka cece ni.
But thou, O Eternal Lord, deal with me for the sake of thy name: because thy kindness is good, deliver thou me.
22 Gama ni matalauci ne mai bukata kuma, zuciyata kuwa ta yi rauni a cikina.
For poor and needy am I, and my heart is deeply wounded within me.
23 Na ɓace kamar inuwar yamma; ana kakkaɓe ni kamar fāra.
Like the shadow when it declineth do I hasten away: I am driven suddenly off like the locusts.
24 Gwiwoyina suna mutuwa saboda azumi; jikina ya rame ba kuma ƙarfi.
My knees stumble through fasting, and my flesh faileth of fatness.
25 Na zama abin dariya ga masu zargina; sa’ad da suka gan ni, suka kaɗa kawunansu.
And I am become a reproach unto them: when they see me, they shake their head.
26 Ka taimake ni, ya Ubangiji Allahna; ka cece ni bisa ga ƙaunarka.
Help me, O Lord my God: O save me according to thy kindness:
27 Bari su san cewa hannunka ne, cewa kai ne, ya Ubangiji, ka yi shi.
That they may know that this is thy hand: that thou, Lord, hast truly done it.
28 Za su iya la’anta, amma kai za ka sa albarka; sa’ad da suka tasar za su sha kunya, amma bawanka zai yi farin ciki.
Let them then curse, but do thou bless: when they arise, let them be made ashamed; but let thy servant rejoice.
29 Masu zargina za su sha kunya za a rufe su da kunya kamar mayafi.
Let my accusers be clothed with confusion, and let them wrap themselves, as with a mantle, in their own shame.
30 Da bakina zan ɗaukaka Ubangiji sosai; cikin babban taro zan yabe shi.
I will thank the Lord greatly with my mouth, and in the midst of many will I praise him.
31 Gama yana tsaya a hannun damar mai bukata, don yă cece ransa daga waɗanda suke hukunta shi.
For he ever standeth at the right hand of the needy, to save him from those that judge his soul.