< Zabura 109 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda. Zabura ce. Ya Allah, wanda nake yabo, kada ka yi shiru,
For the Chief Musician. A Psalm of David. Hold not thy peace, O God of my praise;
2 gama mugaye da masu ruɗu sun buɗe bakunansu a kaina; sun yi magana a kaina da harsunan ƙarya.
For the mouth of the wicked and the mouth of deceit have they opened against me: They have spoken unto me with a lying tongue.
3 Da kalmomin ƙiyayya sun kewaye ni; sun tasar mini ba dalili.
They have compassed me about also with words of hatred, And fought against me without a cause.
4 A maimakon ƙauna sun sāka mini da zargi, amma ni mutum ne mai addu’a.
For my love they are my adversaries: But I [give myself unto] prayer.
5 Sun sāka mini alheri da mugunta, ƙauna kuma da ƙiyayya.
And they have rewarded me evil for good, And hatred for my love.
6 Ka naɗa mugun mutum yă yi hamayya da shi; bari mai zargi yă tsaya a hannun damansa.
Set thou a wicked man over him; And let an adversary stand at his right hand.
7 Sa’ad da aka yi masa shari’a, bari a same shi da laifi, bari kuma addu’o’insa su hukunta shi.
When he is judged, let him come forth guilty; And let his prayer be turned into sin.
8 Bari kwanakinsa su zama kaɗan; bari wani yă ɗauki wurinsa na shugabanci.
Let his days be few; [And] let another take his office.
9 Bari’ya’yansa su zama marayu matarsa kuma gwauruwa.
Let his children be fatherless, And his wife a widow.
10 Bari’ya’yansa su zama masu yawo suna bara; bari a yi ta koransu daga gidajensu da suke kufai.
Let his children be vagabonds, and beg; And let them seek [their bread] out of their desolate places.
11 Bari mai binsa bashi yă ƙwace dukan abin da yake da shi; bari baƙi su washe amfanin aikinsa.
Let the extortioner catch all that he hath; And let strangers make spoil of his labor.
12 Bari kada kowa yă yi masa alheri ko yă ji tausayin marayunsa.
Let there be none to extend kindness unto him; Neither let there be any to have pity on his fatherless children.
13 Bari duk zuriyarsa su mutu, a shafe sunayensu daga tsara mai zuwa.
Let his posterity be cut off; In the generation following let their name be blotted out.
14 Bari a tuna da laifin kakanninsa a gaban Ubangiji; bari kada a taɓa shafe zunubin mahaifiyarsa.
Let the iniquity of his fathers be remembered with Jehovah; And let not the sin of his mother be blotted out.
15 Bari zunubansu su kasance a gaban Ubangiji kullum, don yă sa a manta da su daga duniya.
Let them be before Jehovah continually, That he may cut off the memory of them from the earth;
16 Gama bai taɓa yin tunanin yin alheri ba, amma ya tsananta wa matalauta da mabukata da kuma masu fid da zuciya har suka mutu.
Because he remembered not to show kindness, But persecuted the poor and needy man, And the broken in heart, to slay [them].
17 Yana jin daɗin la’antarwa, bari yă dawo a kansa; ba ya son sa albarka, bari kada kowa yă sa masa albarka.
Yea, he loved cursing, and it came unto him; And he delighted not in blessing, and it was far from him.
18 Ya sa la’antarwa kamar rigarsa; ta shiga cikin jikinsa kamar ruwa, cikin ƙasusuwansa kamar mai.
He clothed himself also with cursing as with his garment, And it came into his inward parts like water, And like oil into his bones.
19 Bari tă zama kamar mayafin da aka ɗaura kewaye da shi, kamar ɗamara da aka ɗaura kewaye da shi har abada.
Let it be unto him as the raiment wherewith he covereth himself, And for the girdle wherewith he is girded continually.
20 Bari wannan yă zama sakayyar Ubangiji ga masu zargina, ga waɗanda suke mugayen maganganu a kaina.
This is the reward of mine adversaries from Jehovah, And of them that speak evil against my soul.
21 Amma kai, ya Ubangiji Mai Iko Duka, ka yi da ni da kyau saboda sunanka; ta alherin ƙaunarka, ka cece ni.
But deal thou with me, O Jehovah the Lord, for thy name’s sake: Because thy lovingkindness is good, deliver thou me;
22 Gama ni matalauci ne mai bukata kuma, zuciyata kuwa ta yi rauni a cikina.
For I am poor and needy, And my heart is wounded within me.
23 Na ɓace kamar inuwar yamma; ana kakkaɓe ni kamar fāra.
I am gone like the shadow when it declineth: I am tossed up and down as the locust.
24 Gwiwoyina suna mutuwa saboda azumi; jikina ya rame ba kuma ƙarfi.
My knees are weak through fasting; And my flesh faileth of fatness.
25 Na zama abin dariya ga masu zargina; sa’ad da suka gan ni, suka kaɗa kawunansu.
I am become also a reproach unto them: When they see me, they shake their head.
26 Ka taimake ni, ya Ubangiji Allahna; ka cece ni bisa ga ƙaunarka.
Help me, O Jehovah my God; Oh save me according to thy lovingkindness:
27 Bari su san cewa hannunka ne, cewa kai ne, ya Ubangiji, ka yi shi.
That they may know that this is thy hand; [That] thou, Jehovah, hast done it.
28 Za su iya la’anta, amma kai za ka sa albarka; sa’ad da suka tasar za su sha kunya, amma bawanka zai yi farin ciki.
Let them curse, but bless thou: When they arise, they shall be put to shame, But thy servant shall rejoice.
29 Masu zargina za su sha kunya za a rufe su da kunya kamar mayafi.
Let mine adversaries be clothed with dishonor, And let them cover themselves with their own shame as with a robe.
30 Da bakina zan ɗaukaka Ubangiji sosai; cikin babban taro zan yabe shi.
I will give great thanks unto Jehovah with my mouth; Yea, I will praise him among the multitude.
31 Gama yana tsaya a hannun damar mai bukata, don yă cece ransa daga waɗanda suke hukunta shi.
For he will stand at the right hand of the needy, To save him from them that judge his soul.

< Zabura 109 >