< Zabura 109 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda. Zabura ce. Ya Allah, wanda nake yabo, kada ka yi shiru,
(Til Sangmesteren. Af David. En Salme.) Du min Lovsangs Gud, vær ej tavs!
2 gama mugaye da masu ruɗu sun buɗe bakunansu a kaina; sun yi magana a kaina da harsunan ƙarya.
Thi en gudløs, svigefuld Mund har de åbnet imod mig, taler mig til med Løgntunge,
3 Da kalmomin ƙiyayya sun kewaye ni; sun tasar mini ba dalili.
med hadske Ord omringer de mig og strider imod mig uden Grund;
4 A maimakon ƙauna sun sāka mini da zargi, amma ni mutum ne mai addu’a.
til Løn for min Kærlighed er de mig fjendske, skønt jeg er idel Bøn;
5 Sun sāka mini alheri da mugunta, ƙauna kuma da ƙiyayya.
de gør mig ondt for godt, gengælder min Kærlighed med Had.
6 Ka naɗa mugun mutum yă yi hamayya da shi; bari mai zargi yă tsaya a hannun damansa.
Straf ham for hans Gudløshed, lad en Anklager stå ved hans højre,
7 Sa’ad da aka yi masa shari’a, bari a same shi da laifi, bari kuma addu’o’insa su hukunta shi.
lad ham gå dømt fra Retten, hans Bøn blive regnet for Synd;
8 Bari kwanakinsa su zama kaɗan; bari wani yă ɗauki wurinsa na shugabanci.
hans Livsdage blive kun få, hans Embede tage en anden;
9 Bari’ya’yansa su zama marayu matarsa kuma gwauruwa.
hans Børn blive faderløse, hans Hustru vorde Enke;
10 Bari’ya’yansa su zama masu yawo suna bara; bari a yi ta koransu daga gidajensu da suke kufai.
hans Børn flakke om og tigge, drives bort fra et øde Hjem;
11 Bari mai binsa bashi yă ƙwace dukan abin da yake da shi; bari baƙi su washe amfanin aikinsa.
Ågerkarlen rage efter alt, hvad han har, og fremmede rane hans Gods;
12 Bari kada kowa yă yi masa alheri ko yă ji tausayin marayunsa.
ingen være langmodig imod ham, ingen ynke hans faderløse;
13 Bari duk zuriyarsa su mutu, a shafe sunayensu daga tsara mai zuwa.
hans Afkom gå til Grunde, hans Navn slettes ud i næste Slægt:
14 Bari a tuna da laifin kakanninsa a gaban Ubangiji; bari kada a taɓa shafe zunubin mahaifiyarsa.
lad hans Fædres Skyld ihukommes hos HERREN, lad ikke hans Moders Synd slettes ud,
15 Bari zunubansu su kasance a gaban Ubangiji kullum, don yă sa a manta da su daga duniya.
altid være de, HERREN for Øje; hans Minde vorde udryddet af Jorden,
16 Gama bai taɓa yin tunanin yin alheri ba, amma ya tsananta wa matalauta da mabukata da kuma masu fid da zuciya har suka mutu.
fordi det ej faldt ham ind at vise sig god, men han forfulgte den arme og fattige og den, hvis Hjerte var knust til Døde;
17 Yana jin daɗin la’antarwa, bari yă dawo a kansa; ba ya son sa albarka, bari kada kowa yă sa masa albarka.
han elsked Forbandelse, så lad den nå ham; Velsignelse yndede han ikke, den blive ham fjern!
18 Ya sa la’antarwa kamar rigarsa; ta shiga cikin jikinsa kamar ruwa, cikin ƙasusuwansa kamar mai.
Han tage Forbandelse på som en Klædning, den komme som Vand i hans Bug, som Olie ind i hans Ben;
19 Bari tă zama kamar mayafin da aka ɗaura kewaye da shi, kamar ɗamara da aka ɗaura kewaye da shi har abada.
den blive en Dragt, han tager på, et Bælte, han altid bærer!
20 Bari wannan yă zama sakayyar Ubangiji ga masu zargina, ga waɗanda suke mugayen maganganu a kaina.
Det være mine Modstanderes Løn fra HERREN, dem, der taler ondt mod min Sjæl.
21 Amma kai, ya Ubangiji Mai Iko Duka, ka yi da ni da kyau saboda sunanka; ta alherin ƙaunarka, ka cece ni.
Men du, o HERRE, min Herre, gør med mig efter din Godhed og Nåde, frels mig for dit Navns Skyld!
22 Gama ni matalauci ne mai bukata kuma, zuciyata kuwa ta yi rauni a cikina.
Thi jeg er arm og fattig, mit Hjerte vånder sig i mig;
23 Na ɓace kamar inuwar yamma; ana kakkaɓe ni kamar fāra.
som Skyggen, der hælder, svinder jeg bort, som Græshopper rystes jeg ud;
24 Gwiwoyina suna mutuwa saboda azumi; jikina ya rame ba kuma ƙarfi.
af Faste vakler mine Knæ, mit Kød skrumper ind uden Salve;
25 Na zama abin dariya ga masu zargina; sa’ad da suka gan ni, suka kaɗa kawunansu.
til Spot for dem er jeg blevet, de ryster på Hovedet, når de
26 Ka taimake ni, ya Ubangiji Allahna; ka cece ni bisa ga ƙaunarka.
Hjælp mig, HERRE min Gud, frels mig efter din Miskundhed,
27 Bari su san cewa hannunka ne, cewa kai ne, ya Ubangiji, ka yi shi.
så de sander, det var din Hånd, dig, HERRE, som gjorde det!
28 Za su iya la’anta, amma kai za ka sa albarka; sa’ad da suka tasar za su sha kunya, amma bawanka zai yi farin ciki.
Lad dem forbande, du vil velsigne, mine uvenner vorde til Skamme, din Tjener glæde sig;
29 Masu zargina za su sha kunya za a rufe su da kunya kamar mayafi.
lad mine Fjender klædes i Skændsel, iføres Skam som en Kappe!
30 Da bakina zan ɗaukaka Ubangiji sosai; cikin babban taro zan yabe shi.
Med min Mund vil jeg højlig takke HERREN, prise ham midt i Mængden;
31 Gama yana tsaya a hannun damar mai bukata, don yă cece ransa daga waɗanda suke hukunta shi.
thi han står ved den fattiges højre at fri ham fra dem, der dømmer hans Sjæl.

< Zabura 109 >