< Zabura 109 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda. Zabura ce. Ya Allah, wanda nake yabo, kada ka yi shiru,
Min Lovsangs Gud, ti ikke!
2 gama mugaye da masu ruɗu sun buɗe bakunansu a kaina; sun yi magana a kaina da harsunan ƙarya.
Thi de have opladt Ugudeligheds Mund og Falskheds Mund imod mig; de have talt imod mig med Løgnens Tunge,
3 Da kalmomin ƙiyayya sun kewaye ni; sun tasar mini ba dalili.
og de have omringet mig med hadefulde Ord og stridt imod mig uden Aarsag.
4 A maimakon ƙauna sun sāka mini da zargi, amma ni mutum ne mai addu’a.
Til Løn for min Kærlighed staa de mig imod, men jeg er stedse i Bøn.
5 Sun sāka mini alheri da mugunta, ƙauna kuma da ƙiyayya.
Og de beviste mig ondt for godt, og Had for min Kærlighed.
6 Ka naɗa mugun mutum yă yi hamayya da shi; bari mai zargi yă tsaya a hannun damansa.
Sæt en ugudelig over ham og lad en Anklager staa ved hans højre Haand!
7 Sa’ad da aka yi masa shari’a, bari a same shi da laifi, bari kuma addu’o’insa su hukunta shi.
Naar han dømmes, da lad ham gaa ud som skyldig, og lad hans Bøn blive tir Synd!
8 Bari kwanakinsa su zama kaɗan; bari wani yă ɗauki wurinsa na shugabanci.
Hans Dage vorde faa, en anden annamme hans Embede!
9 Bari’ya’yansa su zama marayu matarsa kuma gwauruwa.
Hans Børn vorde faderløse og hans Hustru Enke!
10 Bari’ya’yansa su zama masu yawo suna bara; bari a yi ta koransu daga gidajensu da suke kufai.
Og lad hans Børn vanke hid og did og tigge, og lad dem fra deres øde Hjem søge om Føde!
11 Bari mai binsa bashi yă ƙwace dukan abin da yake da shi; bari baƙi su washe amfanin aikinsa.
Lad Aagerkarlen kaste Garn ud efter alt det, han har, og fremmede røve Frugten af hans Arbejde.
12 Bari kada kowa yă yi masa alheri ko yă ji tausayin marayunsa.
Lad ham ikke finde nogen, som bevarer Miskundhed imod ham, og ingen forbarme sig over hans faderløse!
13 Bari duk zuriyarsa su mutu, a shafe sunayensu daga tsara mai zuwa.
Hans Fremtid vorde afskaaren, deres Navn vorde udslettet i andet Led!
14 Bari a tuna da laifin kakanninsa a gaban Ubangiji; bari kada a taɓa shafe zunubin mahaifiyarsa.
Hans Fædres Misgerning vorde ihukommet hos Herren og hans Moders Synd ikke udslettet!
15 Bari zunubansu su kasance a gaban Ubangiji kullum, don yă sa a manta da su daga duniya.
De være Herren altid for Øje, og han udrydde deres Ihukommelse af Jorden;
16 Gama bai taɓa yin tunanin yin alheri ba, amma ya tsananta wa matalauta da mabukata da kuma masu fid da zuciya har suka mutu.
fordi han ikke kom i Hu at gøre Miskundhed, men forfulgte en elendig og en fattig Mand og den, som var bedrøvet i Hjertet, for at dræbe ham.
17 Yana jin daɗin la’antarwa, bari yă dawo a kansa; ba ya son sa albarka, bari kada kowa yă sa masa albarka.
Han elskede Forbandelse, den kom ogsaa over ham, og han havde ikke Lyst til Velsignelse, og den blev ogsaa langt fra ham.
18 Ya sa la’antarwa kamar rigarsa; ta shiga cikin jikinsa kamar ruwa, cikin ƙasusuwansa kamar mai.
Og han iførte sig Forbandelse som sit Klædebon, og den kom ind i ham som Vand og som Olie i hans Ben.
19 Bari tă zama kamar mayafin da aka ɗaura kewaye da shi, kamar ɗamara da aka ɗaura kewaye da shi har abada.
Den vorde ham som et Klædebon, hvilket han ifører sig, og som et Bælte, hvilket han altid ombinder sig med.
20 Bari wannan yă zama sakayyar Ubangiji ga masu zargina, ga waɗanda suke mugayen maganganu a kaina.
Dette er Lønnen fra Herren til dem, som staa mig imod, og som tale ondt imod min Sjæl!
21 Amma kai, ya Ubangiji Mai Iko Duka, ka yi da ni da kyau saboda sunanka; ta alherin ƙaunarka, ka cece ni.
Men du, Herre, Herre! gøre vel imod mig for dit Navns Skyld; red mig, fordi din Miskundhed er god.
22 Gama ni matalauci ne mai bukata kuma, zuciyata kuwa ta yi rauni a cikina.
Thi jeg er elendig og fattig, og mit Hjerte er saaret inden i mig.
23 Na ɓace kamar inuwar yamma; ana kakkaɓe ni kamar fāra.
Jeg svinder bort som en Skygge, naar den hælder, jeg bliver jaget bort som en Græshoppe.
24 Gwiwoyina suna mutuwa saboda azumi; jikina ya rame ba kuma ƙarfi.
Mine Knæ rave af Faste, og mit Kød er magert og har ingen Fedme.
25 Na zama abin dariya ga masu zargina; sa’ad da suka gan ni, suka kaɗa kawunansu.
Og jeg maa være deres Spot; de se mig, de ryste med deres Hoved.
26 Ka taimake ni, ya Ubangiji Allahna; ka cece ni bisa ga ƙaunarka.
Hjælp mig, Herre, min Gud! frels mig efter din Miskundhed,
27 Bari su san cewa hannunka ne, cewa kai ne, ya Ubangiji, ka yi shi.
at de maa kende, at dette er din Haand; du, Herre! du har gjort det.
28 Za su iya la’anta, amma kai za ka sa albarka; sa’ad da suka tasar za su sha kunya, amma bawanka zai yi farin ciki.
Forbande de, saa velsigner du, de rejse sig, men blive til Skamme, og din Tjener glædes.
29 Masu zargina za su sha kunya za a rufe su da kunya kamar mayafi.
Lad mine Modstandere iføres Forsmædelse og klædes med deres Skam som med en Kappe.
30 Da bakina zan ɗaukaka Ubangiji sosai; cikin babban taro zan yabe shi.
Jeg vil takke Herren højlig med min Mund, og jeg vil love ham midt iblandt mange;
31 Gama yana tsaya a hannun damar mai bukata, don yă cece ransa daga waɗanda suke hukunta shi.
thi han staar ved den fattiges højre Haand for at frelse ham fra dem, som dømme hans Sjæl.

< Zabura 109 >